An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato
Published: 7th, August 2025 GMT
’Yan bindiga ɗauke da makamai sun shiga ƙauyen Bimasa a Ƙaramar Hukumar Tureta a Jihar Sakkwato sun kashe mutum huɗu sun jikkata wasu da dama a daren ranar Laraba.
Ɗaya daga cikin jagorori a ƙauyen ya yi wa Aminiya ƙarin bayani ya ce, a daren ranar Laraba da ƙarfe 12:40 na tsakar dare ɓarayi suka shigo ƙauyen akan babura suna da yawa sun fi mutum 10 a nan take suka riƙa harbi kan mai uwa da wabi kai tsaye suka harbe mutum biyar, huɗu suka rasu an kai ɗaya asibiti.
“A haka suka rika harbi ta ko’ina, sun buge shagunan mutane suka kwashe wayoyi a wurin masu caji, shagunan da ke sayar da abinci suka saci abinci da yawa, a lokacin ba su yi garkuwa da kowa ba, suka tafi abinsu.”
Ya ce, a dukkan Ƙaramar hukumar ’yan bindigar sun matsa musu kan haka a yanzu sama da gari 17 duk sun tashi sun dawo cikin hedikwatar Ƙaramar hukumar ta Tureta a Kudu da Arewa duk an bar noma domin tsoron ’yan bindigar kana zuwa gona ana sace ka.
” A yanzu garin Kwarare da Gidan Batare da Kaura da Galadimawa, Ci da sha da Rafin gora da Kuruwa Birni, Dantayawa da sauransu, ba kowa ‘yan bindiga ke yadda suke so a wuraren.”.
Ya roƙi shugaban Ƙaramar hukuma da su yi wata hoɓɓasa da jami’an tsaro don ganin an samu sauƙi musamman mutane na yin noma.
A kullum mutanen yankin cikin fargaba suke ta ‘yan bindiga, abin tausayi da zaran Magrib ta doso mutane za su fara barin gidajensu zuwa wani wurin ɓoyo don kawai su tsira daga harin ’yan bindiga, koyaushe haka ake ya kamata gwamnati ta yi wani abu a lamarin.
Wata majiyar ta ce, sun kashe mutane huɗu, amma sun jikkata mutane sun fi 20 wasu na asibitin Tureta wasu na gida suna jinya.
Ya ce, shugaban ƙaramar hukumar Honarabul Abubakar Aliyu Tureta ya jajanta masu kan halin da ya same su tare da alkawarin tallafawa waɗanda suka samu rauni a harin.
Wakilinmu ya tuntuɓi shugaban Ƙaramar hukumar Tureta kan lamarin, amma ba a samu magana da shi ba domin ba ya kusa da waya a lokacin da aka kira shi kuma bai mayar da amsar saƙon da aka tura masa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sakkwato Ƙaramar hukumar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a Sakkwato
Akalla magidanta 50 ne ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu a kauyuka uku na karamar hukumar Tangaza da ke jihar Sakkwato, sakamakon wani mamakon ruwan sama da aka tafka a yankunan.
Ambaliyar da ta mamaye kauyukan na Tangaza ne da suka hada da Gidan Madi da Baidi da Madarare, kuma ta haifar da rushewar gidaje da lalacewar gonaki da rijiyoyi da sauran su.
Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4 Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin LegasMutanen da lamarin ya shafa sun ce suna bukatar agajin gaggawa na abinci da magani da tsaftataccen ruwan sha.
Shugaban karamar hukumar ta Tangaza, Isah Salihu Kalenjeni, ya jagoranci wata tawaga sun ziyarci wuraren da lamarin ya shafa don ganin barnar da ambakiyar ta yi tare da jajanta wa mutanen yankunan.
A yayin ziyarar, Shugaban karamar hukumar ya tabbatar wa mutanen zai sanar da duk wata hukuma da ta dace don kawo masu daukin gaggawa kan halin da suke ciki.
Hukumomi a karamar hukuma da masu bayar da agajin gaggawa sun kuma yi kira wadanda iftila’in ya shafa da su yi aiki tukuru don kare barkewar annobar ciwo ga sauran al’umma.
Aliyu Na Abba daya daga cikin mutanen da ambaliyar ta rusa wa gida da gonaki biyu ya ce yana bukatar hukuma ta tausaya masa halin damuwar da shi da iyalansa suka fada.
Umaima Dan Umaru da ta ke da marayu uku a tare da ita ta ce gonakinsu biyu da suka yi shuka sun lalace sabadiyyar ambaliyar, don haka suna neman agaji.
Ta ce akalla akwai kusan mutum 50 da suka tafka asara a yankin nasu.