Aminiya:
2025-11-08@14:22:52 GMT

An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato

Published: 7th, August 2025 GMT

’Yan bindiga ɗauke da makamai sun shiga ƙauyen Bimasa a Ƙaramar Hukumar Tureta a Jihar Sakkwato sun kashe mutum huɗu sun jikkata wasu da dama a daren ranar Laraba.

Ɗaya daga cikin jagorori a ƙauyen ya yi wa Aminiya ƙarin bayani ya ce, a daren ranar Laraba da ƙarfe 12:40 na tsakar dare ɓarayi suka shigo ƙauyen akan babura suna da yawa sun fi mutum 10 a nan take suka riƙa harbi kan mai uwa da wabi kai tsaye suka harbe mutum biyar, huɗu suka rasu an kai ɗaya asibiti.

’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara

“A haka suka rika harbi ta ko’ina, sun buge shagunan mutane suka kwashe wayoyi a wurin masu caji, shagunan da ke sayar da abinci suka saci abinci da yawa, a lokacin ba su yi garkuwa da kowa ba, suka tafi abinsu.”

Ya ce, a dukkan Ƙaramar hukumar ’yan bindigar sun matsa musu kan haka a yanzu sama da gari 17 duk sun tashi sun dawo cikin hedikwatar Ƙaramar hukumar ta Tureta a Kudu da Arewa duk an bar noma domin tsoron ’yan bindigar kana zuwa gona ana sace ka.

” A yanzu garin Kwarare da Gidan Batare da Kaura da Galadimawa, Ci da sha da Rafin gora da Kuruwa Birni, Dantayawa da sauransu, ba kowa ‘yan bindiga ke yadda suke so a wuraren.”.

Ya roƙi shugaban Ƙaramar hukuma da su yi wata hoɓɓasa da jami’an tsaro don ganin an samu sauƙi musamman mutane na yin noma.

A kullum mutanen yankin cikin fargaba suke ta ‘yan bindiga, abin tausayi da zaran Magrib ta doso mutane za su fara barin gidajensu zuwa wani wurin ɓoyo don kawai su tsira daga harin ’yan bindiga, koyaushe haka ake ya kamata gwamnati ta yi wani abu a lamarin.

Wata majiyar ta ce, sun kashe mutane huɗu, amma sun jikkata mutane sun fi 20 wasu na asibitin Tureta wasu na gida suna jinya.

Ya ce, shugaban ƙaramar hukumar Honarabul Abubakar Aliyu Tureta ya jajanta masu kan halin da ya same su tare da alkawarin tallafawa waɗanda suka samu rauni a harin.

Wakilinmu ya tuntuɓi shugaban Ƙaramar hukumar Tureta kan lamarin, amma ba a samu magana da shi ba domin ba ya kusa da waya a lokacin da aka kira shi kuma bai mayar da amsar saƙon da aka tura masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakkwato Ƙaramar hukumar yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

 Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe

A yau Juma’a ne dai masu shigar da kara a Tanzania su ka gabatar da tuhumar mutane da dama da zargin cin amanar kasa, saboda rawar da su ka taka a cikin rikicin zaben shugaban kasa.

 Mutane 76 ne aka tuhuma da cewa; Sun yi kokarin kawo cikas akan zaben da aka yi a ranar 29 ga watan Oktoba da kuma tsokanar mahukunta a birnin Darussalam.

Baya ga laifin cin amanar kasa,ana kuma tuhumar mutanen da cewa sun kitsa aikata laifuka.

Zaben da aka yi a kasar Tanzani a karshen watan Oktoba, ya bar baya da kura saboda tashe-tashen hankulan da aka samu.

Babbar jam’iyyar adawa ta Chadema ta yi zargin cewa an kashe mutane fiye da 1,000,kuma a halin yanzu mahukuntan suna kokari boye duk wata shaida ta laifukan da su ka aikata ta hanyar binne gawawwaki a asirce.

Wadanda su ka sanya idanu a yadda aka gudanar da zaben sun ce, da akwai rashin gaskiya akan yadda aka gudanar da shi.

Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan wacce ta hau karagar Mulki a 2021 bayan rasuwar magabacinta, ta lashe zaben da kawo 97% kamar yadda mahukuntan kasar su ka sanar.

Manyan ‘yan hamayya a zaben shugaban kasar da su ne Tundu Lissu daga jam’iyyar Chadema, da luhaga Mpina na jam’iyyar ACT-Wazalendo, an hana su shiga zaben da aka gudanar. Tarayyar Afirka ta ce masu sa ido da ta aike sun bayyana mata cewa;zaben bai hau ma’auninta na inganci ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Limamin Juma’ar Tehran: Tsayin Dakan ‘Yan Gwagwarmaya Daga Koyi Ne Da Alkur’ani Mai Girma November 7, 2025 Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan November 7, 2025  Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan November 7, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  •  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku a Kudancin Lebanon  
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano