Dakarun da ke karkashin sashe na 3 na OPSH, da aka tura wurin da lamarin ya faru, biyo bayan kiran gaggawa da aka yi musu, sun tabbatar da cewa, makiyayan sun riga sun yanka shanun da kansu, domin gudun kar a yi asara da yawa. Binciken da aka yi a yankin ya kai ga gano tumatur da ake zargin guba ne da yalon lambu an warwatsa a filin.

Kuma babu gidaje a kusa da wurin, wanda hakan ke haifar da zargin cewa, mai yiwuwa wasu da ba a san ko su waye ba ne suka ajiye abun wanda ake kyautata zaton yana dauke da guba.

 

A martanin da babban jami’in runduna ta 3 kuma kwamandan OPSH, ya jagoranci wata tawaga mai karfi da suka hada da shugaban karamar hukumar Bassa, jami’in ‘yansanda na shiyya, da sauran masu ruwa da tsaki zuwa wurin domin ganewa idanunsu. Ziyarar ta kwantar da yiwuwar tarzoma tare da dakile duk wani harin ramuwar gayya daga al’ummar Fulanin da abin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran

Tawagar jami’ai da ‘yan kasuwan kasar Tunisiya ta gana da mataimakin shugaban kasar Iran

A yayin ganawarsa da ministan kasuwanci da fitar da kayayyaki na kasar Tunisiya Samir Ben Salem Obeid, mataimakin shugaban kasar Iran na farko na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: Lokaci ya yi da za a dauki kwararan matakai wajen fadada dangantakar tattalin arziki tsakanin Iran da Tunusiya.

A yayin taron, wanda aka gudanar a ofishinsa tare da halartar jakadan kasar Tunisiya a Iran Imed Rahmouni da tawagar da ke tare da shi, Aref ya bayyana cewa, dangantakar siyasa da ke tsakanin al’ummar Iran da Tunisiya na tafiya cikin wani yanayi mai ma’ana, amma hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ya kasance kasa da abin da ake bukata, bisa la’akari da dama da karfin da bangarorin biyu ke da shi.

A yayin ganawar, Aref ya tunatar da ziyarar da ya kai birnin Qairawan na kasar Tunusiya shekaru ashirin da suka gabata, lokacin da ya rike mukamin mataimakin shugaban kasar na farko na Jamhuriyar. Ya kara da cewa a lokacin yana jin kamar ya ratsa daya daga cikin garuruwan Khorasan na kasar Iran, yana daukar birnin Qairawan wata alama ce ta hadin kan al’ummar musulmi da alakar al’adu da addini tsakanin Iran da Tunisiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi