Dakarun da ke karkashin sashe na 3 na OPSH, da aka tura wurin da lamarin ya faru, biyo bayan kiran gaggawa da aka yi musu, sun tabbatar da cewa, makiyayan sun riga sun yanka shanun da kansu, domin gudun kar a yi asara da yawa. Binciken da aka yi a yankin ya kai ga gano tumatur da ake zargin guba ne da yalon lambu an warwatsa a filin.

Kuma babu gidaje a kusa da wurin, wanda hakan ke haifar da zargin cewa, mai yiwuwa wasu da ba a san ko su waye ba ne suka ajiye abun wanda ake kyautata zaton yana dauke da guba.

 

A martanin da babban jami’in runduna ta 3 kuma kwamandan OPSH, ya jagoranci wata tawaga mai karfi da suka hada da shugaban karamar hukumar Bassa, jami’in ‘yansanda na shiyya, da sauran masu ruwa da tsaki zuwa wurin domin ganewa idanunsu. Ziyarar ta kwantar da yiwuwar tarzoma tare da dakile duk wani harin ramuwar gayya daga al’ummar Fulanin da abin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi ikirarin cewa akwai mutanen da ke aiki a matsayin ‘yan leken asiri ga ‘yan ta’adda da suka hada da Sojoji, ‘yan siyasa da sauran mutanen gari. Da yake jawabi yayin hira da kamfanin labarai na ‘News Central’ a ranar Laraba, gwamnan ya jaddada bukatar sabunta dabarun leken asiri da daukar kwararan matakai don magance matsalar rashin tsaro a yankin. Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna “Akwai wadanda suka yi hadin gwiwa da ‘yan ta’adda daga cikin sojojin Nijeriya, cikin ‘yan siyasa, da kuma cikin mazauna yankunanmu, abin da za mu yi shi ne mu karfafa fasahar leken asirinmu don cafko marasa kishin kasa acikinmu sannan mu yi maganinsu ba tare da wani tausayi ba” in ji Zulum. Ya yi kira da a sauya salon yaki da matsalar tsaro, yana mai yin Allah wadai da irin wannan kwangila da wasu ke amsowa don tada zaune tsaye. A cewarsa, kawar da irin wadannan mutane, na iya maido da zaman lafiya cikin gaggawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin
  • ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 
  • Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum
  • Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar
  • Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto