Gwamnatin Jihar Jigawa ta biya iyalai 14 da aikin sake gina Babban Masallacin Gumel ya shafa kudaden diyya da suka kai Naira miliyan 277 da dubu 44.

An gudanar da bikin bayar da takardun cekin kudin ne a Fadar Mai Martaba Sarkin Gumel, Dr. Ahmad Muhammad Sani, tare da halartar masu rike da sarautu, da shugabannin al’umma da manyan jami’an gwamnati.

Da yake jawabi yayin bikin, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, wanda Babban Sakataren Harkokin Gudanarwa da Kudi na Ofishinsa, Alhaji Abdullahi Sa’idu, ya wakilta, ya shawarci iyalan da su yi amfani da kudaden ta hanya mai amfani wajen gina sabbin gidajensu tare da rungumar sauyin wurin zama cikin hakuri da tawakkali.

Malam Bala Ibrahim ya jaddada cewa an aiwatar da tsarin biyan diyyar bisa adalci da gaskiya domin tabbatar da cewa kowa ya samu hakkinsa yadda ya dace.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Gumel, Hon. Muhammad Gako, ya yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa wannan karamci, yana mai tabbatar da goyon bayan karamar hukumar wajen nasarar aikin sake gina masallacin.

An bayar dda kudaden diyyar ne domin rage wa iyalan da abin ya shafa radadin sauyin da suka fuskanta tare da bayar da damar ci gaba da aikin sake gina masallacin cikin lumana.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Diyya Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar

Gwamnatin Najeriya ta jaddada matsayinta na yin watsi da ayyata a matsayin kasa mai take hakkokin addinai da Amurka ta yi.

Da yake kare tarihin Najeriya, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Ƙasa na Najeriya, Mohammed Idris, ya ce “barazanar Trump na ɗaukar matakin soja ba ta da tushe kuma hakan yana a matsayin kawar da ido ne daga ƙalubalen tsaro masu sarkakiya da Najeriya ke fuskanta,” ya ƙara da cewa “duk wani labari da ke nuna cewa Najeriya ta gaza ɗaukar mataki kan hare-haren da ake kai wa mabiya addini ya dogara ne akan bayanan ƙarya ko maganganu marasa tushe.”

A ranar Litinin, Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Olufemi Oluwedi, ya bayyana cewa “Najeriya tana fuskantar ta’addanci, ba kai hari ko cin motuncin Kiristoci ba,” kuma “shugabancin Najeriya yana maraba da taimakon Amurka wajen yaƙi da ta’addanci matuƙar tana mutunta haƙƙinta na yankuna.”

Idris ya ƙara da cewa gwamnatinsu ta samu ci gaba mai yawa a yaƙi da ta’addanci tun bayan hawanta mulki a watan Mayun 2023, yana mai cewa “kofar gwamnatin Najeriya ta kasance a buɗe kuma tana son yin aiki kafada da kafada da gwamnatin Amurka da sauran ƙasashe da abokan hulɗa don cimma burin kawar da ta’addanci gaba ɗaya a ƙasar Najeriya.”

Idris ya jaddada cewa “ta’addanci ya shafi Kiristoci da Musulmai,” kuma gwamnati ta kuduri aniyar kawo ƙarshen ayyukan masu tsattsauran ra’ayi ta hanyar ɗaukar matakan soja, haɗin gwiwa a yanki, da tattaunawa da abokan hulɗa na duniya.

A makon da ya gabata, Shugaban Amurka Donald Trump ya mayar da Najeriya cikin jerin ƙasashen da Amurka ta ce suna take ‘yancin addini. A ranar Asabar, ya ce ya umarci Ma’aikatar Tsaro da ta shirya don yiwuwar ɗaukar matakin soja cikin gaggawa idan Najeriya ba ta ɗauki mataki mai tsauri kan kisan Kiristoci ba. Matakin da Washington ta ɗauka ya kawo cikas ga dangantakar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar  Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE  Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi  November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 China ta yi alkawarin ci gaba da tallafawa Najeriya bayan barazanar Trump November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
  • GORON JUMA’A
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
  • Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140