A kokarin ta na ci gaba da inganta ayyukan ta, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta gudanar da bitar sanin makamar aiki ga malaman bita na kananan hukumomin jihar 27.

Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo wanda ya jagoranci gudanar ta taron a shelkwatar hukumar dake Dutse, ya ce an shirya taron ne domin nusar da malaman ayyukan daya rataya a kawunan su domin cimma burin da aka sanya a gaba.

A cewar sa, hukumar zata sanya malaman bitar a cikin kwamitocin hukumar daban-daban domin samun nasarar gudanar da aikin hajjin bana.

Yana mai cewar, a matsayin su na jagororin maniyata aikin hajji, akwai bukatar su kasance da maniyata tare da fadakar dasu akan aikin hajjin da zasu gudanar a kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo

Alhaji Ahmed Umar Labbo, yace tuni hukumar ta karbi fasfo na maniyata kuma sun shigar dasu cikin runbun yin biza.

Kazalika, Labbo yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da gwamnatin jihar ta dauki nauyin malaman bita zuwa aikin hajjin bana domin hidimtawa maniyatan aikin hajjin bana.

A nasa tsokacin, Daraktan fadakarwa da wayar da kai na hukumar, Alhaji Abdullahi Aliyu, yayi jawabi ga malaman bitar kan nauyin da ya rataya a kawunan su.

Yana mai kira a gare su dasu sadaukar kai domin taimakawa maniyyata a kowanne fannin da hukumar ta umarce su domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Wasu daga cikin malaman bitar da suka zanta da Radio Nigeria,sun yabawa Gwamna Umar Namadi da shugaban hukumar alhazai ta jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da daukar nauyin su domin jagorantar maniyatan aikin hajjin wannan shekarar.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Bitar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

Majalisar ta kuma umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) da ta samar da kayayyakin agaji ga al’ummomin da hare-haren ya shafa domin bayar da agajin jin-kai.

 

Da yake gabatar da kudirin, Sanata Abbas, ya ce hare-haren da aka kai sun raba dubban mazauna karamar hukumar ta Hong da gidajensu, tare da lalata musu rayuwa.

 

Ya yi nuni da cewa, sake bullar ‘yan ta’addan ya zarce Adamawa hat zuwa jihohin Borno da Yobe, lamarin da ya kara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin Arewa maso Gabas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa
  • Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano
  • DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”
  • Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  • Malamai sun gindaya sharaɗi kafin janye yajin aiki a Abuja 
  • Maniyatan Jigawa 550 Sun Isa Kasa Mai Tsaki Don Aikin Hajjin Bana
  • Gwamnatin Kebbi Ta Naɗa Sabbin Sakatarorin Kananan Hukumomi
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20