A kokarin ta na ci gaba da inganta ayyukan ta, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta gudanar da bitar sanin makamar aiki ga malaman bita na kananan hukumomin jihar 27.

Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo wanda ya jagoranci gudanar ta taron a shelkwatar hukumar dake Dutse, ya ce an shirya taron ne domin nusar da malaman ayyukan daya rataya a kawunan su domin cimma burin da aka sanya a gaba.

A cewar sa, hukumar zata sanya malaman bitar a cikin kwamitocin hukumar daban-daban domin samun nasarar gudanar da aikin hajjin bana.

Yana mai cewar, a matsayin su na jagororin maniyata aikin hajji, akwai bukatar su kasance da maniyata tare da fadakar dasu akan aikin hajjin da zasu gudanar a kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo

Alhaji Ahmed Umar Labbo, yace tuni hukumar ta karbi fasfo na maniyata kuma sun shigar dasu cikin runbun yin biza.

Kazalika, Labbo yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da gwamnatin jihar ta dauki nauyin malaman bita zuwa aikin hajjin bana domin hidimtawa maniyatan aikin hajjin bana.

A nasa tsokacin, Daraktan fadakarwa da wayar da kai na hukumar, Alhaji Abdullahi Aliyu, yayi jawabi ga malaman bitar kan nauyin da ya rataya a kawunan su.

Yana mai kira a gare su dasu sadaukar kai domin taimakawa maniyyata a kowanne fannin da hukumar ta umarce su domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Wasu daga cikin malaman bitar da suka zanta da Radio Nigeria,sun yabawa Gwamna Umar Namadi da shugaban hukumar alhazai ta jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da daukar nauyin su domin jagorantar maniyatan aikin hajjin wannan shekarar.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Bitar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.

A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar.

Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar.

Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin kafa 3,000 da 2,500, kuma yana ɗauke da kusan rumfuna 1,000 na wucin gadi, inda rumfuna 529 suka ƙone ƙurmus.

Sai dai ya tabbatar cewa ba a rasa rai ba a wannan hatsari.

Ya danganta musabbabin gobarar da aikace-aikacen wasu mutane masu shaye-shaye da ke zaune a cikin kasuwar.

Mai magana da yawun hukumar ya shawarci jama’a da ’yan kasuwa da su kasance masu hankali da taka-tsantsan wajen amfani da wuta da abubuwan da ke iya kama da wuta, domin kauce wa irin wannan ibtila’i a nan gaba.

Khadijah Aliyu

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Karfafa Dangantaka Da NAFDAC
  • DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna
  • Babban Lauyan Jihar Kwara Ya Tabbatar da Gudanar da Adalci da Kare Hakkokin Mace
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas
  • Jerin ’yan wasan da ke takarar lashe kyautar gwarzon Afirka na bana
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Sanar Da Wa’adin Biyan Kafin Alkalami Na Shekarar 2026
  • Jihar Kwara Ta Ware Naira Biliyan 8 Don Biyan Haƙƙin Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Biliyan Daya Wajen Gyaran Ajujuwa A Makarantu