Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
Published: 17th, April 2025 GMT
A kokarin ta na ci gaba da inganta ayyukan ta, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta gudanar da bitar sanin makamar aiki ga malaman bita na kananan hukumomin jihar 27.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo wanda ya jagoranci gudanar ta taron a shelkwatar hukumar dake Dutse, ya ce an shirya taron ne domin nusar da malaman ayyukan daya rataya a kawunan su domin cimma burin da aka sanya a gaba.
A cewar sa, hukumar zata sanya malaman bitar a cikin kwamitocin hukumar daban-daban domin samun nasarar gudanar da aikin hajjin bana.
Yana mai cewar, a matsayin su na jagororin maniyata aikin hajji, akwai bukatar su kasance da maniyata tare da fadakar dasu akan aikin hajjin da zasu gudanar a kasa mai tsarki.
Alhaji Ahmed Umar Labbo
Alhaji Ahmed Umar Labbo, yace tuni hukumar ta karbi fasfo na maniyata kuma sun shigar dasu cikin runbun yin biza.
Kazalika, Labbo yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da gwamnatin jihar ta dauki nauyin malaman bita zuwa aikin hajjin bana domin hidimtawa maniyatan aikin hajjin bana.
A nasa tsokacin, Daraktan fadakarwa da wayar da kai na hukumar, Alhaji Abdullahi Aliyu, yayi jawabi ga malaman bitar kan nauyin da ya rataya a kawunan su.
Yana mai kira a gare su dasu sadaukar kai domin taimakawa maniyyata a kowanne fannin da hukumar ta umarce su domin kwalliya ta biya kudin sabulu.
Wasu daga cikin malaman bitar da suka zanta da Radio Nigeria,sun yabawa Gwamna Umar Namadi da shugaban hukumar alhazai ta jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da daukar nauyin su domin jagorantar maniyatan aikin hajjin wannan shekarar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bitar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
Kotu ta yanke wa wani wanda ya yi wa wata yarinya ’yar shekara 12 fyaɗe hukuncin ɗaurin rai-da-rai a Ƙaramar Hukumar Guba ta Jihar Yobe.
Babbar Kotun Jihar Yobe da ke zaune a ƙaramar hukumar Gujba ta yanke wa mutumin mai shekaru 31 mai suna Ali Kwano.
An gurfanar da shi ne a kan zargin ya kai yarinyar cikin aji a ƙaramar makarantar sakandare ta je-ka-ka-dawo da ke garin Bumsa, inda ya yi lalata da ita da ƙarfi.
Ya yaudari yarinyar ce bayan ya gaya mata cewa ta jira shi a cikin aji bisa cewar zai sayi ƙosai.
Bayan da ta shiga ajin sai ya kama hannunta, ya rufe bakinta ya danne ta a ƙasa sannan ya yi lalata da ita da ƙarfi.
Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh Gumi ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a KanoAlƙaliyar da ke jagorantar shari’a, Mai Shari’a Amina Shehu, ta same shi da laifi, don haka ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai bisa ga sashe na 3 na dokar haramta cin zarafin mutane, ta Jihar Yobe ta Shekarar 2020.