Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
Published: 17th, April 2025 GMT
A kokarin ta na ci gaba da inganta ayyukan ta, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta gudanar da bitar sanin makamar aiki ga malaman bita na kananan hukumomin jihar 27.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo wanda ya jagoranci gudanar ta taron a shelkwatar hukumar dake Dutse, ya ce an shirya taron ne domin nusar da malaman ayyukan daya rataya a kawunan su domin cimma burin da aka sanya a gaba.
A cewar sa, hukumar zata sanya malaman bitar a cikin kwamitocin hukumar daban-daban domin samun nasarar gudanar da aikin hajjin bana.
Yana mai cewar, a matsayin su na jagororin maniyata aikin hajji, akwai bukatar su kasance da maniyata tare da fadakar dasu akan aikin hajjin da zasu gudanar a kasa mai tsarki.
Alhaji Ahmed Umar Labbo
Alhaji Ahmed Umar Labbo, yace tuni hukumar ta karbi fasfo na maniyata kuma sun shigar dasu cikin runbun yin biza.
Kazalika, Labbo yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da gwamnatin jihar ta dauki nauyin malaman bita zuwa aikin hajjin bana domin hidimtawa maniyatan aikin hajjin bana.
A nasa tsokacin, Daraktan fadakarwa da wayar da kai na hukumar, Alhaji Abdullahi Aliyu, yayi jawabi ga malaman bitar kan nauyin da ya rataya a kawunan su.
Yana mai kira a gare su dasu sadaukar kai domin taimakawa maniyyata a kowanne fannin da hukumar ta umarce su domin kwalliya ta biya kudin sabulu.
Wasu daga cikin malaman bitar da suka zanta da Radio Nigeria,sun yabawa Gwamna Umar Namadi da shugaban hukumar alhazai ta jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da daukar nauyin su domin jagorantar maniyatan aikin hajjin wannan shekarar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bitar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fara ɗaukar likitoci da sauran ma’aikatan lafiya domin aikin Hajji da ke tafe a ƙasar Saudiyya.
Hukumar NAHCON ta bayyana cewa shafin neman aikin ya fara aiki daga ƙarfe 11 na dare ranar Juma’a 12 ga Nuwamba, 2025. Za a rufe shafin da ƙarfe 11.59 ranar Litinin, 15 ga watan Disamba, 2025
Latsa nan domin shiga shafin ɗaukar ma’aikatan lafiyan kai-tsaye.
NAHCON ta bayyana cewa jami’an lafiyan da za a ɗauka Su ƙunshi likitoci, masu haɗa magunguna, malaman jinya, da jami’an kula da lafiyar lafiya da ta muhalli (CHO/EHO). Su ne za su yi aikin kula da lafiyar alhazai a yayin aikin Hajjin na shekarar 2026.
NAHCON ta bayyana cewa jami’an da suka yi aiki da ita a matsayin kula da lafiyar alhazai a shekaru uku da suka gabata (2023 zuwa 2025) ba ne kaɗai za a ɗauka domin wannan aiki na 2026.
Yadda za ku nemi aikinMasu nema za su shiga shafinta kai-tsaye domin ganin ka’idodin da kuma cike bayanansu. Latsa nan domin lafiyan kai-tsaye.
Ko kuma su gaida babban shafinta daga nan su latsa wasu layuka huɗu da ke hannun dama daga sama.
Daga daga nan su latsa RESOURCES, sai su latsa su shiga NMT Application Portal.
A ciki za su ga ka’idodin neman aikin, su cike bayansu, da kuma sauke duk dakardun da su cike.
Hukumar NAHCON ta bayyana cewa daga bisani za a tuntuɓi duk waɗanda suka yi nasara.
Allah Ya ba da sa’a.
Ka’idodin neman aikinNAHCON ta jaddada cewa:
– Ma’aikatan lafiya da suka cancanta ne kawai za su iya nema aikin ba Tawagar Lafiya ta Ƙasa (NMT) domin aikin Hajjin 2026
– Aikin NMT na 2026 zai gudana ne bisa tsarin sa-kai, bisa ƙa’idojin duniya da NAHCON ta amince da su.
– Bayanai da aka bayar za su taimaka wajen tantance cancanta da shirin shiga matakin gaba na tantancewa ko jarabawa.
– Duk bayanan da aka gabatar za a duba su. Duk wani kuskure. Ɓoye gaskiya, ko ƙirƙirar bayanan ƙarya zai iya jawo ƙin amincewa da aikace-aikacen ko cirewa daga jerin waɗanda cancanta.
– Wannan aikace-aikacen kyauta ne gaba ɗaya. NAHCON ba ta karɓar kuɗi kai tsaye ko a kaikaice, ko ta hannun wakilai ko hukumomi. Ku yi hattara!
– Cika fom ɗin ba ya nufin an amince da cancanta ko zaɓen ku.
Ƙa’idar shekaru:
– Likitoci: 27 zuwa 60 shekara
– Masu haɗa Magunguna: shekara 26 zuwa 60
– Nas da sauran rukuni: 22–60 shekara .
SharuɗɗaDole masu neman shiga NMT su kasance:
1. Suna aiki a lokacin neman shiga.
2. Ba su halarci ayyukan NMT a shekara uku da suka gabata ba (2023, 2024, da 2025).
3. Su kasance a shirye su yi aiki na tsawon kwanaki 28 da kuma zama a Saudiyya har zuwa kwanaki 45 kafin dawowa Najeriya.
4. Ba za a sallame su a wurin aikinsu ba kafin su kammala aikin NMT.
5. Su nuna kyawawan halaye tare da bin ƙa’idojin aikin lafiya da na NAHCON.
6. Su gabatar da tabbacin mai tsaya musu (guarantor).
Sharuɗɗan Guarantor:
– Dole ya kasance mutum mai daraja: Ma’aikacin gwamnati (ba ƙasa da GL 15), basaraken gargajiya, Alƙali (Magistrate), ko Shugaban Ƙaramar Hukuma.
– Dole ya san mai neman aikin NMT tsawon aƙalla shekaru biyar kuma ya tabbatar da gaskiya, ƙwarewa, da iya aikinsa.
– Dole ya gabatar da kwafin katin shaida ko wata takardar shaida da ake amfani da ita a ofisoshin gwamnati na Najeriya.
Takardun da dole a haɗa da su:
– Fom ɗin Guarantor da aka cika
– Takardar shaidar ƙwarewar aiki (Basic Professional Certificate)
– Takardar NYSC (idan ta shafi mai nema)
– Lasisin aikin lafiya na wannan shekara
– Hoton fasfo (mai farin baya)
– Sanarwar mai nema (applicant’s declaration)
– Takardar izini daga wurin aiki (employer’s clearance letter) .