Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.

 

Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.

 

Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.

 

“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”

 

Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.

 

Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da wannan cuta

এছাড়াও পড়ুন:

Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano

Ana fargabar cewa wasu yara biyu sun riga mu gidan gaskiya bayan faɗawa rijiya a ƙananan hukumomin Dawakin Tofa da Dala da ke Jihar Kano.

Mai magana da yawun Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu

A cewarsa, tsautsayin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 8:53 na safiyar ranar Talata a ƙauyen Kashirmo da ke yankin Sarkakiya na Dawakin Tofa, inda wata yarinya mai shekara takwas mai suna Zara’u Muhammad ta faɗa wata rijiya da ke kusa da gidansu.

Duk da ƙoƙarin jama’a na ceto yarinyar kafin isowar jami’an hukumar kashe gobara ya ci tura, saboda zurfin rijiyar da kuma yawan ruwan da ke cikinta.

Sai dai daga bisani an tsamo gawarta, sannan aka miƙa ta ga dagacin yankin, Abdullahi Garba.

Sai kuma a Larabar ce makamancin wannan lamari ya auku, inda wani yaro mai shekara shida, Ahmad Abdurashid, ya faɗa rijiya a unguwar Dandishe Tsamiyar Goodluck da ke a ƙaramar hukumar Dala.

An dai samu nasarar ceto yaron a raye amma daga bisani ya ce ga garinku nan.

Daraktan hukumar, Alhaji Sani Anas, ya bayyana baƙin ciki kan faruwar irin waɗannan lamurra, yana mai roƙon jama’a da su riƙa rufe rijiyoyi da kyau da kuma kula da yara ƙanana domin guje wa irin wannan mummunan sakamako.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Genoa ta naɗa Daniele De Rossi sabon kociya
  • A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano