Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
Published: 7th, August 2025 GMT
Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.
Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.
Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.
“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”
Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.
Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: da wannan cuta
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta kama mutum biyar da ake zargi da satar fakiti 7,871 na abincin yara, wanda aka fi sani da Tamuwa, wanda aka tanada don yara masu fama da cutar yunwa.
Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar 19 ga Satumba, 2025 .
Ya bayyana cewa an gano kayan ne a samame guda biyu da aka kai a Maiduguri.
Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a EnuguSamamen farko ya auku ne a ranar 12 ga Afrilu, lokacin da aka tsayar da wata mota a Njimtilo, kusa da Maiduguri, inda aka gano fakiti 3,314 na Tamuwa, wanda hakan ya sa aka kama mutum biyu.
Haka kuma, a ranar 9 ga watan Yuni, jami’an tsaro sun tsayar da wata mota a Legacy Estate, Maiduguri, inda aka gano ƙarin fakiti 4,557.
Wannan ya kai ga kama wasu mutum uku da ake zargi.
ASP Daso ya ce: “’Yan sanda ba za su lamunci karkatar da kayayyakin agaji ba, domin an tanade su ne don ceton rayuka, musamman na marasa galihu.”
An miƙa kayan da aka ƙwato ga gwamnatin Jihar Borno, ta hannun Kwamishinan Lafiya, Farfesa Baba Mallum Gana, domin raba su yadda ya dace.
A halin yanzu, an gurfanar da mutane biyar da aka kama a gaban kotu domin fuskantar hukunci.