Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
Published: 7th, August 2025 GMT
Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.
Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.
Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.
“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”
Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.
Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: da wannan cuta
এছাড়াও পড়ুন:
An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama wasu bama-bamai da ba su fashe ba da wasu tarin makamai da aka shigar da su jihar cikin kayan gwangwan daga jihar Borno.
Lamarin dai ya jefa fargaba a zukatan mutane kan yadda kayayyaki ke yawo babu bincike daga jihohin da ke fama da rikici.
Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi IIKakakin rundunar a jihar, DSP Mansir Hassan ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce an kama kayan ne ranar Asabar bayan wasu bayanan sirri da rundunar ta samu.
Ya ce an samu kayan ne a cikin wani kamfanin da ke hada-hadar kayan gwangwan da ke rukunin masana’antu na Kudandan da ke karamar hukumar Kaduna ta Kudu.
“Wasu kwararrun jami’anmu daga sashen da ke kula da abubuwa masu fashewa ne ya je wajen bayan bayanan. Bayan cikakken bincike, an tabbatar da cewa kayan bama-bamai ne da ba su kai ga fashewa ba,” in ji Mansir.
Kakakin ya ce nan take jami’an nasu suka kwashe bama-baman zuwa wajen da ya dace sannan suka lalata su ba tare da sun fashe ba.
Ya kuma ce yayin aikin, dakarun sun gano makamai, cikin har da wata karamar bindiga kirar gida wacce ke makare da albarusai, da ma wasu tarin makaman.
Kakakin ya ce nan take Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabiu Muhammad ya bayar da umarnin rufe kamfanin da aka sami kayan domin a samu damar fitar da dukkan makaman ba tare da an bar ragowa ba.
Kwamishinan ya kuma gargadi masu sana’ar ta gwangwan da su daina kawo irin kayayyakin daga yankunan da suke fama da rikici zuwa jihar ta Kaduna.
Ya kuma ce yanzu haka suna ci gaba da bincike domin gano tushen makaman da kuma dalilin shigo da su cikin jihar.