Aminiya:
2025-11-08@15:47:09 GMT

Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore

Published: 7th, August 2025 GMT

Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.   Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba.

.   A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya   Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.   Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.   Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.   Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.   Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

“A yayin da ake tarwatsa masu kai harin, DPO na Sassan A da B sun tura ma’aikatansu suka harba hayaki mai sa hawaye, amma wasu motoci cikin motar gwamnan sun lalace,” in ji Abiodun.

Ya bayyana cewa mutane uku na farko da ake zargi sune Ali Mohammed da Adamu Hussain, dukkansu daga yankin Nasarafu, Bida, da Isah Umaru na yankin Darachita, Bida. Ya kara da cewa an kama Nagenu, mai shekaru 39, daga yankin Bello Masaba, daga baya dangane da wannan lamari, sannan ya ambaci wasu biyu, Salihu Mohammed da Abdulrahman Baba, yayin tambayoyi.

“Dukkan wadanda ake zargi suna karkashin bincike kuma suna taimaka wa ‘yansanda wajen gano wasu. Ana ci gaba da kokarin kama karin mutane da ake zargi,” in ji Abiodun.

Lauyan Nagenu, Barrister Ibrahim Wali, ya kuma tabbatar da kama abokin aikinsa ga *Daily Trust*, yana cewa ana tsare da shi a Ofishin Rundunar ‘Yan Sanda na Yanki a Bida. Ya bayyana cewa kama shi na da alaka da bidiyon da ya bazu, kuma ana daukar matakan shari’a don samun ‘yancinsa.

Kokarin tuntubar jami’an NNPP bai samu nasara ba. Kiran da aka yi ga shugaban jam’iyyar na jihar, Danladi Umar Abdulhamid, bai yi nasara ba, kuma bai amsa sakonnin da aka tura masa ba.

Gwamnatin Neja ta yi alkawarin gurfanar da masu laifi a gaban shari’a

Babban Mataimakin Musamman ga Gwamna kan Tattara Matasa, Hamza Bida, ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar an hukunta wadanda suka yi wannan hari.

Yayin da yake magana da Daza TB, wata kafar yada labar ta Hausa, ya ce wannan lamari ba shi da alaka da zaben kananan hukumomi.

“Ban ji dadi da abin da wadannan yara suka yi a Bida ba. Abin da ya faru shi ne, a rana daya kafin zaben, mutane sun taru a gidan gwamna kuma ya yi musu alkawarin ba su kudi a ranar Lahadi. Daga baya daren nan, an kafa wani kwamitin, ciki har da dan majalisar wakilai na Bida/Gbako/Katcha, don tabbatar da cewa kudin ya isa ga kowa,” in ji Bida.

Ya kara da cewa wasu matasa, wadanda ba su gamsu da tsarin ba, suka rikide zuwa tashin hankali. “Wadanda suka yi wannan aikatawa yara ne da iyayensu suka rasa ikon kula da su, amma za mu koya musu darasi,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki November 7, 2025 Labarai Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja November 7, 2025 Manyan Labarai Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Babban Matsalar Jin Kai A Falasdinu, Inda Falasdinawa Miliyan 1.5 Suke Cikin Halin Musiba Da Bala’i
  • Ajax ta kori kocinta John Heitinga
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano