Aminiya:
2025-08-07@13:18:57 GMT

Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore

Published: 7th, August 2025 GMT

Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.   Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba.

.   A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya   Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.   Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.   Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.   Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.   Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa

Kungiyar masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da kishin kasa reshen jihar Nasarawa ta kalubalanci kungiyar tabbatar da gaskiya da rikon amana da shugabanci na gari (NS-TA&G), da su tabbatar da zargin nuna son kai wajen sauke nauyin da babban Akanta Janar na jihar, Ahmed Musa Mohammed ke yi.

 

Ko’odinetan kungiyar na jiha Abimiku Dangana Solomon ne ya bayyana hakan a lokacin da yake mayar da martani ga wani jawabi da Mista Lazarus Salaki, ko’odinetan kungiyar NS-TA&G2 na jihar ya yi a wani taron manema labarai da aka gudanar a garin Lafia babban birnin jihar.

 

Mista Abimiku Dangana ya ce, hukuncin da kotun koli ta yanke na baya-bayan nan bai hana masu rike da mukaman gwamnati da ma’aikatan gwamnati shiga harkokin siyasa da shiga jam’iyyun siyasa ba.

 

Kungiyar ta kuma bayyana cewa, shari’ar INEC  da Ahmed Musa inda mai shari’a Ayoola da Justice Mohammad Uwais suka jaddada cewa dokokin ma’aikatan ba za su iya maye gurbin tanadin tsarin mulki ba.

 

“Muna kalubalantar Hukumar NS-TA&G2 da ta ba da shaidar nuna fifiko na musamman da ake zargin an yi mata ko kuma an yi kasa a gwiwa wajen sauke nauyin da Akanta Janar na Jiha ke yi.

 

Idan za a iya tunawa wata kungiyar da abin ya shafa a karkashin Mista Lazarus Salaki, ta yi kira ga Mista Musa Ahmed Mohammed, Akanta Janar na Jihar Nasarawa ya yi murabus, bisa zarginsa da hannu a harkokin siyasa yayin da yake rike da wani mukami mai muhimmanci.

 

Kungiyar ta kuma bayar da misali da umarnin da tsohon sakataren gwamnatin jihar, Mohammed Uban-doma Aliyu ya bayar a ranar 16 ga Afrilu, 2024, inda ya umurci duk masu rike da mukaman siyasa masu burin shiga zabe da su yi murabus ko kuma su dakatar da harkokin siyasa har sai Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC ta bayyana matsayarta.

 

Mista Lazarus Salaki ya yi zargin cewa, duk da wannan umarnin, wasu da aka nada sun ci gaba da yakin neman zabe da kuma gudanar da taron siyasa yayin da suke kan mukamansu.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
  • Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
  • An soka wa jami’in Sibil Difens wuka har lahira a Jigawa
  • LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa