Aminiya:
2025-09-24@11:18:35 GMT

Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore

Published: 7th, August 2025 GMT

Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.   Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba.

.   A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya   Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.   Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.   Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.   Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.   Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI

Hukumar da ke kula da yi wa Kamfanoni Rajista ta Najeriya (CAC) ta ƙaddamar da sabon shafin intanet mai amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira wato AI domin sauƙaƙa rajistar harkokin kasuwanci da kamfanoni a Najeriya.

Shugaban Hukumar, Hussaini Ishaq Magaji (SAN), ne ya bayyana a yayin taron masu ruwa da tsaki da hukumar ta shirya a Kano ranar Litinin.

Dalilin da muke goyon bayan tsare-tsaren Tinubu na karɓo bashi — Majalisar Wakilai Sarkin Ruman Katsina ya rasu

Ya kuma ce hukumar ta kawo sabbin sauye-sauye da za su inganta ayyukanta da kuma sauƙaƙa wa ’yan kasuwa yin rajista da ita.

Magaji ya ce, “Ko ina kake, daga dakinka, ba tare da ka san kowa a CAC ba, kuma ba tare da biyan kowa komai ba, za ka iya yin rajistar sunan kasuwancinka ka samu takardar shaidarka cikin ƙasa da minti 10.”

“Adadin bayanan da shafinmu na intanet ke ɗauka ya tashi daga 3.5TB zuwa kusan 12TB cikin watanni uku da fara jagorancin hukumar,” in ji shi.

Shugaban ya kuma ce hukumar na karɓar saƙon imel sama da 3,000 a kullum, yayin da ma’aikata ƙasa da 100 ke kula da su da kuma bayar da amsa.

Sai dai ya ce sabon shafin da aka ƙaddamar, zai karanta kuma ya rarraba tare da bayar da amsa ga dubban sakonnin na imel cikin daƙiƙa daya.

Ya kuma ce karfin aikin shafin wanda aka fara amfani da shi a watan Yuni ba shi da iyaka.

Hussaini ya ce, “Babu inda a duniya ake yin rajistar sunan kasuwanci cikin ƙasa da minti 10. Mu ne muka fara, sauran su biyo baya.

“A yau kaɗai, akwai aƙalla kamfanoni 7,000 da ke buƙatar a yi musu rijista, yayin da ma’aikata 63 ne kawai ke aikin. Wannan ne ya sa dole mu fara amfani da wannan fasahar domin inganta ayyukanmu,” in ji shi.

Ana sa ran shugaban hukumar zai gabatar da jawabi kan nasarorin da hukumar ta samu a fasahar a yayin taron hukumomin da ke kula da yi wa kamfanoni rajista na duniya da za a yi a ƙasar Tunisia wata mai zuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • Mahara sun kashe ɗan sanda, sun ɗauke bindigarsa a Taraba
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a Kogi
  • SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno