Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
Published: 7th, August 2025 GMT
Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
Wata kungiyar matasa, Kauru Youth Ambassadors (KYA) a karamar hukumar Kauru sun nuna matukar damuwa kan yadda Barnabas Danmaigona, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kauru a majalisar dokokin jihar Kaduna, ya gaza samar da ingantaccen wakilci tun bayan zaben sa.
A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai taken daga ‘Daga Fata zuwa Yaudara’ wanda kuma Junaidu Ishaq Maisalati, ya sanyawa hannu, kungiyar ta caccaki dan majalisar kan abin da ta bayyana a matsayin mai dimama kujera kuma ɗan siyasar da ya gaza wajen gudanar da ayukka a mazabar da kuma aikin da zai amfani al’umma.
Sanarwar ta koka da yadda al’ummar Kauru suka sanya kyakkyawan fata a shugabancin Danmaigona, amma a maimakon haka, ya kasa ba marada kunya.
Har ila yau, ta yi Allah-wadai da kawancen siyasarsa da Mukhtar Chawai, wani dan siyasa da aka ce ko ake zargin baya tabuka komai a mazabarsa ba, tare da bayyana cewa irin wannan kawancen yana kashe musu gwiwa matukar gaske.
KYA ta bayyana rashin jin dadin ta a kan abin da suka kira wasu ‘yan kudaden da basu gaza dubu 5 zuwa 10 da yake rabawa jama’a a matsayin yankawa kare ciyawa domin wannan ba abin da suke tsinanawa al’ummar da yake wakilta
Saboda haka Kungiyar ta bukaci al’ummar mazabar Kauru da su tashi tsaye akan nuna halin ko-in-kula a siyasance, su nemi wakilcin da ya dace, sannan su ki yarda a ba su kyauta irin wannan da bata tsinana musu komai.
Sun yi nuni da ‘yan majalisa irin su Hon. Shehu Yunusa na Kubau, wanda rahotanni suka ce ya ba da fifiko wajen hada kai da ci gaba, a matsayin misalan yadda wakilci na gaskiya ya kasance.
Da take kira da a wayar da kan ‘yan siyasa da kuma daukar matakin gama gari, sanarwar ta kalubalanci matasa da masu kada kuri’a a Kauru da su yi wa shugabanninsu hisabi, inda ta dage cewa zabe aiki ne..
KYA ta bayyana cewa Hon. Danmaigona ya samu damarsa, kuma har yanzu jama’a na nan suna jira, ba wai kawai alkawura ba, a’a, a samu canji na zahiri.
Rel/Yusuf Zubairu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Sabo da irin mawuyacin halin da ake ciki ta fannin tsarin jagorancin duniya musamman a daidai wannan lokaci, ya sa shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorancin duniya a kwanakin baya, shawarar da ta yi nuni da cewa, ya kamata a tsaya tsayin daka a kan kin yarda da daukar matakai na kashin kai, tare da kiyaye matsayin MDD, don ta taka rawar da ba wanda zai iya maye gurbinta a cikin tsarin jagorancin duniya. Lallai kasar Sin ta gabatar da shawarar, musamman don neman dakile ayyukan nuna fin karfi da ake fama da su a duniya, tare da samar da mafita ga kasa da kasa da suka shiga duhu.
A sati mai zuwa, za a gudanar da babbar muhawara da ma babban taron tabbatar da shirin samar da kasashe biyu a yayin babban zauren MDD, kafin haka, manyan kawayen Amurka irinsu Birtaniya da Faransa cewa suka yi za su amince da kafuwar kasar Palasdinu, lamarin da ya sake shaida cewa, babu wanda zai iya hana adalci. Lokacin da Amurka ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa, ba yarjejeniyar zaman lafiya kadai ta jefa cikin kwadon shara ba, har da matsayinta na jagorancin duniya.
Tabbas “komai nisan dare gare zai waye”, duk duhun da Gaza ke ciki, haske zai bayyana. Fatan kasa da kasa na wanzar da zaman lafiya zai kai ga kawar da dukkan abubuwan da ke tarnaki tare da shimfida dauwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, wanda hakan zai bude mana sabon babin tsarin jagorancin duniya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp