Hukumar NDLEA ta Nijeriya da takwararta ta Indiya sun amince da yin aiki tare domin daƙile safarar miyagun ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu. Wannan yarjejeniya ta fito ne daga wata tattaunawa ta kafar intanet tsakanin Shugaban NDLEA na Nijeriya, Janar Buba Marwa (mai ritaya), da shugaban hukumar ta Indiya, Anurag Garg.

Shugabannin sun jaddada buƙatar haɗin gwuiwa, musamman wajen hana shigo da haramtattun magunguna daga Indiya zuwa Nijeriya. Marwa ya ce akwai buƙatar a ƙarfafa wannan dangantaka bisa yarjejeniyar da aka rattaba wa hannu a shekarar 2023.

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

Buba Marwa ya roƙi hukumar Indiya da ta tallafa wa NDLEA ta hanyar bai wa jami’anta horo na musamman domin inganta dabarunsu wajen yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi.

Nijeriya na daga cikin ƙasashen da ke fama da matsalar shaye-shaye da safarar miyagun ƙwayoyi, wanda hakan ya sa aka kafa NDLEA domin daƙile wannan barazana ga lafiyar jama’a da zaman lafiya a ƙasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya

Wata yarinya ’yar shekara 17, Nafisa Abdullah, daga Jihar Yobe, ta lashe Babbar Gasar Harshen Turanci ta Duniya ta ‘TeenEagle’ ta shekarar 2025 da aka gudanar a birnin Landan, fadar gwamnatin  ƙasar Birtaniya.

Nafisa ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 ce baya da ta fafata ne da sama da mahalarta gasar 20,000 daga ƙasashe kusan 69 na duniya, inda ta zama ta ɗaya a Gasar ‘UK Global Finals’, sakamakon fintinkau da ta yi wa takwarorinta na ƙasashe daban-daban da ke jin harshen Ingilishi a duniya.

Wannan nasara ta lashe wannan babbar gasa da Nafisa ta samu ya haifar da alfahari a faɗin Najeriya, musamman a mahaifarta, Jihar Yobe. Nafisa ta wakilci Najeriya ne daga Kwalejin Tulip International College (NTIC), Jihar Yobe.

A wani jawabi da ya gabatar jim kaɗan da sanarwar lashe gasar, wani ɗan uwan Nafisa, Malam Hassan Salihu, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Yobe da Makarantar NTIC bisa irin gudunmawar da suna bayar har ya kai ga samun nasarar ’yar uwarsa a wannan babbar gasa ta duniya. Ya ƙara da yaba wa shugabannin kwalejin bisa ga yadda suke gudanar da karatuttukansu da hakan ne ta kai ga nasarar.

Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta

“Tabbas wannan nasara da Nafisa ta samu da taimakon Allah (SWT) ne,” in ji shi, kuma nasarar wata babbar shaida ce ga abin da matasan Najeriya za su iya cimma idan aka ba su dama da goyon baya.

“Alal haƙiƙa wannan nasara da Nafisa ta samu ya zama abin farin ciki da alfahari ga duk al’ummar jiharmu ta Yobe da ma ƙasa baki daya,” in ji Malam Hassan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
  • Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
  • Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano
  • Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya
  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu