Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
Published: 7th, August 2025 GMT
Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Qasa sun kutsa inda Hukumar ‘Yan sanda ta Qasa ke tsare xan gwagwarmayar neman haqqin bil’Adama Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da qarfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.
Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da qarfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a qoqarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba..
jiya Laraba ne dai Sowore ya masa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na Qasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaqa da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya da kuma zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Qasa ya qara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa qa’ida ba.
Sai dai xan rashin kare haqqin xan’Adan xin ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a natsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don xauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na Qasa Kayode Egbetokun da kuma Hukumar ‘Yansada ta Qasa ke aikatawa.
Tuni dai Qungiyar Kare Haqqin Bil’Adama ta Duniya wato Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Nijeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sava wa ‘yancinsa na faxain albakacin bakinsa.
Haka kuma Amnesty International ya buqaci a sake Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuxxa ba.
Shi ma Dakta Bello Galadanci xan gwagwarmayar rajin kare haqqin xan’Adama da aka fi sani da suna Xan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook inda ya ce, “ana tsare mutum ba bisa ka’ida ba, sai a kuma karya masa hannu? A tafi da shi kamar dabba ba tare da sanar da danginsa ko lauyoyinsa ba?
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
“A wani ɓangare na wannan dubarar, jam’iyyar a ƙarƙashin kulawar ɗaya daga cikin manyan ma’aikatan gwamnati, ta yi ƙoƙarin shirya zaɓen jagoranci ƙungiyar Musulmai ƴ an asalin Jihar Filato a cibiyar Azi Nyako da ke Dadin-Kowa a garin Jos, wanda daga bayanan da aka samu lamarin ya kasa samun nasara.
“PDP na ganin cewa da wannan dubarar na raba kan Musulmin Jihar Filato za ta iya samun nasara a zaɓen 2027, wanda wannan ka iya kawo rashin jituwa da haɗin kan al’umma, musamman a irin wannan lokaci da ake fama da rikice-rikice addini da ƙabilanci da kuma ayyukan ƴ an ta’adda, wanda hakan bai kamata a siyasantar da addini ba.
“Yadda PDP ke amfani da addini a matsayin hanyar lashe zaɓe, tana sake dawo da amfani da siyasa mara tsafta wajen lashe zaɓen 2027 da kowacce hanya,” in ji mai magana da yawun APC.
Amma shugaban PDP na yankin tsakiyar Nijeriya, Monday Daspan, ya musanta wannan zargin a matsayin wanda ba shi da tushe ballantana makama.
“Bamaiyi ya shigo harkar siyasa ta bayan fage ba hanyar da ya kamata ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa hakan ya yi masa sauƙi wajen gwama addini da harkokin siyasa. Mafi yawan waɗanda suka shigo harkar siyasa ta bayan fage ba su da cikakken ƙwarewa wajen yin magana a cikin harkokin siyasar ƙasar nan.
“Mu a matsayinmu, APC ba za su iya daidaita tsakanin mulki da ci gaba ba. Sun yi rashin nasara kan zaɓe kuma suna son danganta shi da wani abu. Matsalar a nan dai ita ce, Gwamna Celeb Mutfwang yana aiki ko kuma ba ya yi? Eh. Shin Lalong ya yi aiki da ya yi? A’a,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp