Manoma sama da 500 daga gundumomi 15 na karamar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara sun samu horo kan kiwon awaki na zamani da kuma yadda ake samar da abincin dabbobi, a wani yunƙuri na rage yawan rikici tsakanin manoma da makiyaya tare da inganta rayuwar al’ummar karkara.

An gudanar da wannan horo a Idofian karkashin haɗin gwiwar karamar hukumar Ifelodun da shirin Livestock Productivity and Resilience Support Project (L-PRES).

Da yake jawabi a wurin taron, mataimakin gwamnan jihar Kwara, Mista Kayode Alabi wanda Honarabul Ganiyu Afolabi, dan majalisar jihar mai wakiltar mazaɓar Omupo ya wakilta,  ya jaddada muhimmancin wannan shiri wajen magance matsalolin da manoman karkara ke fuskanta. Ya bayyana cewa shirin ba wai kawai zai rage rikici ba ne,  zai kuma ƙara yawan kudaden shiga ga manoma da kuma ƙarfafa cin gashin kansu.

Ya ja hankalin mahalarta da su yi amfani da damar wajen amfani da sabbin ilimin da suka samu domin faɗaɗa sana’arsu da kuma samar da abincin dabbobi cikin sauƙi ta hanyar amfani da shara daga amfanin gona.

Shi ma da yake jawabi, shugaban karamar hukumar Ifelodun, Honarabul Abdulrasheed Yusuf, ya bayyana cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da ayyukan yi da kuma rage kuɗin da ake kashewa wajen kiwon dabbobi ta hanyar samar da abincin dabbobi a cikin gida.

Ya kuma ƙara da cewa karamar hukumar tana aiki tare da masu ruwa da tsaki don samar da muhimman abubuwa kamar ruwa da wasu muhimman abubuwan raya ƙauyuka.

A nasa jawabin, sarkin Igbaja, Oba Ahmed Babalola (Elesie na Igbaja), ya yabawa wadanda suka shirya wannan horo, yana mai cewa an yi shi a  lokacin da ya dace. Ya tabbatar wa  mahalarta  cikakken goyon baya domin nasara da dorewar shirin.

A baya, shugaban shirin L-PRES a jihar Kwara, Mista Olusoji Oyawoye, ya ƙarfafa matasa da su rungumi dama a fannin noma domin su dogara da kansu maimakon jiran aikin gwamnati. Ya buƙaci mahalarta horon da su rungumi shirin da cikakkiyar niyya domin su samu ƙwarewa da za ta taimaka musu da al’ummarsu gaba ɗaya.

Wannan horo wani ɓangare ne na babban shirin L-PRES da ke ƙoƙarin ƙara yawan amfanin kiwo, rage rikice-rikice, da kuma inganta ɗorewar rayuwa a ƙauyuka a faɗin Najeriya.

Ali Muhammad Rabi’u

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

Kwamishinan lafiya na Jihar Adamawa, Dokta Felix Tangwami ya bayyana cewa, cutar kwalara a Ƙaramar hukumar Mubi ta yi sanadin mutuwar mutane 10, inda ya buƙaci mazauna yankin da su kula da tsaftar jikinsu.

Da yake yi wa Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) bayani a Yola ranar Laraba, Tangwami ya ce marasa lafiyan sun mutu ne a gida maimakon a cibiyoyin lafiya.

Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita

Ya ƙara da cewa, gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumar lafiya ta duniya (WHO) sun ɗauki matakin gaggawa don daƙile ɓarkewar cutar.

“Tun daga farko, mun ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin, kasancewar mu a can, kuma ba za a iya musanta hakan ba,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, waɗanda suka ziyarci cibiyoyin kiwon lafiya sun samu kulawa, inda aka kwantar da majinyata 25 a ranar Talata 4 ga watan Nuwamba, yayin da wasu da dama kuma an sallame su tare da wayar da su kan harkokin tsafta.

Ya bayyana cewa, an tura jami’an kula da cututtuka na jihar, da Daraktan kula da cututtuka a Hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko, da masu aikin sa-kai zuwa Mubi domin gudanar da ayyuka da kuma wayar da kan jama’a.

Sun kuma gano waɗanda abin ya shafa a cikin unguwanni don tabbatar da sun samu kulawar lafiya.

Tangwami ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya da su goyi bayan ƙoƙarin gwamnati ta hanyar ƙarfafa gwiwar mazauna yankin da su gaggauta neman magani a cibiyoyin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano