Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta
Published: 17th, April 2025 GMT
Ya bayyana cewa shiga wani yanki da ba a fahimtar yaren juna ɗauke da makamai na iya janyo fargaba da tashin hankali.
“Ka yi tunanin idan wasu daga Kudu sun shigo ƙauyanku ɗauke da makamai kuma ba ku fahimtar yaren juna — za ku ji tsoro. Haka nan idan mutanenmu suka shiga yankin Kudu da makamai, su ma za a ji tsoro,” in ji shi.
Rurum ya ce zai gana da shugabannin ƙungiyoyin masu farauta a jihar domin daƙile wannan ɗabi’a, ya kuma buƙace su da su nemo hanyar nema wa kansu asiri .
“Wasu su tafi farauta su dawo ba tare da sun kamo ko ɓeran daji ba. Bai dace su ci gaba da haka ba. Ya kamata mu nemi wata hanya ta zaman lafiya da kwanciyar hankali,” in ji shi.
Haka kuma, ya bayar da gudunmawar naira miliyan biyar ga iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya sha alwashin gina makaranta a garin domin girmama su.
Rurum ya kuma ce zai haɗa kai da Sanata Kawu Sumaila domin su kai ƙudiri a majalisa a kan kisan da aka yi wa mafarautan jihar a garin Uromi don ganin an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
CP Bakori ya gode wa al’ummar Kano saboda goyon bayan da suke ba su a ƙoƙarin su na yaƙar masu aikata laifuka tare da kira ga ci gaba da haɗin kai wajen kai rahoton abubuwan da suke zargi ga Ƴansanda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp