Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
Published: 7th, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bada motocin aiki ga shugabannin hukumomi, jami’an tsaro da wasu manyan jami’an gwamnati a jihar.
An gudanar da bikin mika motocin ne a Fadar Gwamnati da ke Minna.
Gwamna Bago ya bayyana cewa wannan mataki na bayar da motocin aiki na da nufin tallafa wa harkokin sufuri da kara inganta gudanar da ayyuka yadda ya kamata.
Ya yabawa kwazon wadanda suka amfana da motocin a aikin gwamnati tare da bukatar su yi amfani da su bisa gaskiya da amanar da aka dora musu domin cimma nasarorin da ake bukata.
Cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin akwai Shugabannin Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomi, Hukumar Majalisar Dokoki, Hukumar Ma’aikata da Hukumar Kula da Binciken Kudade.
Sauran sun hada da Darakta Janar na Gyaran Makarantu, Babban Mai Binciken Asusun Kananan Hukumomi da Ma’aikacin Kudi na Fadar Gwamnati.
Gwamnan ya kuma mika karin motocin Hilux guda 20 ga hukumomin tsaro daban-daban domin karfafa ayyukansu a fadin jihar.
Aliyu Lawal.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Borrell: Rashin tabuka komai daga Turai ya karfafa gwiwar Isr’ila wajen aikata laifuka
Tsohon jami’in harkokin wajen Tarayyar Turai Joesp Borrell, ya yi gargadi game da ci gaba da rashin taka rawar gani daga bangaren kasashen Turai dangane da ayyukan cin zarafin da Isra’ila ke ci gaba da yi, yana mai cewa irin wannan rashin hankali ya sa kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta zama abokiyar tarayya a cikin laifukan da Isra’ila ke aikatawa.
Joesp Borrell ya bayyana hakan ne a cikin wani fashin baki wanda aka buga a cikin jaridar The Guardian ta kasar Burtaniya.
“Wadanda ba su yi aiki ba don dakatar da wannan kisan kiyashi da kuma keta dokokin kasa da kasa, duk da cewa suna da ikon yin wani abu kan hakan, to tabbas suna da hannu a cikin wadannan laifuka,” in ji shi.
Borrell ya ba da misali da yakin kisan kiyashi da gwamnatin kasar Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta kaddamar tun daga watan Oktoban 2023 a kan zirin Gaza wanda ya zuwa yanzu ya lakume rayukan Falasdinawa akalla 60,332, galibi mata da kananan yara, a matsayin babban misali.
Tsohon jami’in ya kuma yi tsokaci game da harin da ake kaiwa a matsugunan Falastinawa wa a kullum a yammacin gabar kogin Jordan.
EU, ta sha tabbatar da cewa ita ce babbar abokiyar kasuwanci ta gwamnatin Isra’ila, kuma babban mai saka hannun jari, kuma babban mai samar da makamai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa August 5, 2025 Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka August 5, 2025 Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump August 5, 2025 Hamas ta musanta kalaman Witkoff game da batun mika makamanta August 5, 2025 Araqchi: Namijin kokarin al’ummar Iran abin yabawa ne August 4, 2025 Khatibzadeh: Iran ba za ta amince da saryar da hakkokinta ba a duk wata tattaunawa da Amurka August 4, 2025 Rahotonni: Agajin Jin kai Da Ake Jefawa Ta Sama A Gaza Ba Shi Da Tasiri August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci