Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-08@17:13:02 GMT

Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi

Published: 7th, August 2025 GMT

Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bada motocin aiki ga shugabannin hukumomi, jami’an tsaro da wasu manyan jami’an gwamnati a jihar.

An gudanar da bikin mika motocin ne a Fadar Gwamnati da ke Minna.

Gwamna Bago ya bayyana cewa wannan mataki na bayar da motocin aiki na da nufin tallafa wa harkokin sufuri da kara inganta gudanar da ayyuka yadda ya kamata.

Ya yabawa kwazon wadanda suka amfana da motocin a aikin gwamnati tare da bukatar su yi amfani da su bisa gaskiya da amanar da aka dora musu domin cimma nasarorin da ake bukata.

Cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin akwai Shugabannin Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomi, Hukumar Majalisar Dokoki, Hukumar Ma’aikata da Hukumar Kula da Binciken Kudade.

Sauran sun hada da Darakta Janar na Gyaran Makarantu, Babban Mai Binciken Asusun Kananan Hukumomi da Ma’aikacin Kudi na Fadar Gwamnati.

Gwamnan ya kuma mika karin motocin Hilux guda 20 ga hukumomin tsaro daban-daban domin karfafa ayyukansu a fadin jihar.

Aliyu Lawal.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Tun da farko, Daraktan DSS na Jihar Kaduna, Mr. Hakeem Abiola, an shirya taron ne domin nazarin ƙalubalen aiki da kuma karfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro. Ya bayyana cewa hukumar DSS a ƙarƙashin jagorancin Mr. Oluwatosin Adeola Ajayi tana amfani da dabaru biyu – na ƙarfi da na sulhu – domin tabbatar da zaman lafiya. Ya ƙara da cewa ci gaba da tattaunawa da shugabannin addinai da na al’umma kamar JNI da CAN ya taimaka wajen shawo kan rikice-rikice kafin su zama tashin hankali.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah November 7, 2025 Manyan Labarai Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump November 7, 2025 Manyan Labarai Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari  November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa