’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti
Published: 7th, August 2025 GMT
Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Ekiti, Joseph Eribo, ya tabbatar da ƙwato jaririn da aka sace a wani asibiti da ke Ado-Ekiti ranar Litinin.
An miƙa jaririn ga iyayensa, Mustapha Aliyu mai shekara 29 da kuma Salmatu Lawal mai shekara 22, bayan da jami’an ’yan sanda suka tsananta binciken lamarin.
An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a BornoA cewar Eribo, an samu nasarar ne bayan samun wani sahihin daga wani da ya ba da rahoto ya tuntuɓi wani babban jami’in ‘yan sanda, inda ya nuna shakku kan wata mata da ta yi imanin cewa tana da alaƙa da sace jaririyar da ta ji a cikin labarai.
Binciken da aka yi ya sa jami’an ’yan sanda suka kai gano wata jaka da aka bari a asibiti. Jakar na ƙunshe da ƙullin auduga da kuma takardar shaida daga wani babban kanti.
Hotunan na’urar CCTV daga babban kanti ya nuna wata mata da wasu gungun maza, inda suka taimaka wa ’yan sanda wajen ganowa tare da kama wacce ake zargin.
Rundunar ’yan sandan ta bayyana cewa, wanda ake zargin ta yi ƙaryar tana da juna biyu kuma ta yi kamar tana jiran haihuwa a asibiti. Ta yi amfani da damar da ta samu ta sace jaririn a lokacin da mahaifiyar jaririn ta ɗan tashi daga wajen.
Da take magana da manema labarai, wanda ake zargin Miss Deborah Ayeni, ta amsa laifin da ake zargin ta aikata. Ta ce, ta yi ɓarin cikinta ne a watan Maris kuma tana tsoron mijin nata da ke zaune a Birtaniya zai iya barinta, lamarin da ya sa ta sace jaririn. Ta yarda ta kwana a asibiti tare da ƙulla alaƙa da jaririn kafin ta sace shi.
Mahaifin jaririn, Mustapha Aliyu ya bayyana godiyarsa ga Allah da aka mayar masa da jaririn nasa lafiya, ya kuma yaba wa ’yan sanda bisa gaggawar ɗaukar matakin da suka ɗauka da kuma ƙwazon aiki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
A cewar ‘yansanda, “A ranar 10/10/25, an gayyato wani Mista Oke Emmanuel, dan NYSC kuma abokin dakin wanda ya bace, domin yi masa tambayoyi. Ya tabbatar cewa wanda ake nema ya kasance tare da iyalan George har zuwa 06/10/25.
“An samu karin bayani daga George cewa dan NYSC din ya koka da rashin lafiya, aka kai su Asibitin Kaiama Referral Hospital a ranar 04/10/25, kuma aka sallame shi ranar 05/10/25. Sai dai a ranar 06/10/25, dan NYSC din ya bace zuwa wani wurin da ba a sani ba.”
‘Yansanda kuma suna binciken zargin karbar kudin rashawa na Naira 100,000 daga iyayen wanda ya bace, da wasu fursunoni biyu da ke gidan gyaran hali na Igbara, Abeokuta, Jihar Ogun, wadanda suka yi suna kamar masu garkuwa da mutane.
“An bar wayar salula ta wanda ya bace a dakinsa. Jami’an bincike suka bi layin kira daga lambar 0906193291, inda aka gano tana hannun wani fursuna da ake tsare da shi a cibiyar gyaran hali ta Igbara, Abeokuta, saboda wani laifin garkuwa da mutane.
“Wanda ake zargin ya ce sun ga lambar wayar a kafafen sada zumunta, suka yi amfani da ita don cutar da mahaifin wanda ya bace, Mista Anyanwu Simon, mai shekara 56. An biya kudin Naira 100,000 zuwa asusun Opay mai lamba 7042793493 na wata Atinuke Oluwalose, abokiyar hadin bakin fursunan da ke gidan yarin Abeokuta.”
“Daga bayanan da jami’an bincike suka gano, akwai wasu abubuwan damuwa da ka iya kasancewa silar abin da ya faru. An gano wasu kalaman da wanda ya bace ya yi dangane da wasu sabbin dabi’u da sha’awowi da ba su dace da akidar addininsa ba,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta kammala da cewa ana ci gaba da daukar matakan bincike “domin tabbatar da sakamakon da jami’an bincike suka tattara, kasancewar binciken ya fito da abubuwa masu ban mamaki. Ba a samu wata alamar garkuwa da mutane a wannan lamari ba. Ana ci gaba da aiki domin samun cikakken bincike.”
PUNCH Metro ta ruwaito a watan Oktoba 2024 cewa an kama mutum hudu kan bacewar wani dan NYSC mai suna Yahya Faruk, wanda yake hidima a Ikuru, cikin Karamar Hukumar Andoni ta jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA