Aminiya:
2025-08-07@17:39:00 GMT

’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti

Published: 7th, August 2025 GMT

Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Ekiti, Joseph Eribo, ya tabbatar da ƙwato jaririn da aka sace a wani asibiti da ke Ado-Ekiti ranar Litinin.

An miƙa jaririn ga iyayensa, Mustapha Aliyu mai shekara 29 da kuma Salmatu Lawal mai shekara 22, bayan da jami’an ’yan sanda suka tsananta binciken lamarin.

An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno

A cewar Eribo, an samu nasarar ne bayan samun wani sahihin daga wani da ya ba da rahoto ya tuntuɓi wani babban jami’in ‘yan sanda, inda ya nuna shakku kan wata mata da ta yi imanin cewa tana da alaƙa da sace jaririyar da ta ji a cikin labarai.

Binciken da aka yi ya sa jami’an ’yan sanda suka kai gano wata jaka da aka bari a asibiti. Jakar na ƙunshe da ƙullin auduga da kuma takardar shaida daga wani babban kanti.

Hotunan na’urar CCTV daga babban kanti ya nuna wata mata da wasu gungun maza, inda suka taimaka wa ’yan sanda wajen ganowa tare da kama wacce ake zargin.

Rundunar ’yan sandan ta bayyana cewa, wanda ake zargin ta yi ƙaryar tana da juna biyu kuma ta yi kamar tana jiran haihuwa a asibiti. Ta yi amfani da damar da ta samu ta sace jaririn a lokacin da mahaifiyar jaririn ta ɗan tashi daga wajen.

Da take magana da manema labarai, wanda ake zargin Miss Deborah Ayeni, ta amsa laifin da ake zargin ta aikata. Ta ce, ta yi ɓarin cikinta ne a watan Maris kuma tana tsoron mijin nata da ke zaune a Birtaniya zai iya barinta, lamarin da ya sa ta sace jaririn. Ta yarda ta kwana a asibiti tare da ƙulla alaƙa da jaririn kafin ta sace shi.

Mahaifin jaririn, Mustapha Aliyu ya bayyana godiyarsa ga Allah da aka mayar masa da jaririn nasa lafiya, ya kuma yaba wa ’yan sanda bisa gaggawar ɗaukar matakin da suka ɗauka da kuma ƙwazon aiki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai

Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai

Wata kungiyar matasa, Kauru Youth Ambassadors (KYA) a karamar hukumar Kauru sun nuna matukar damuwa kan yadda Barnabas Danmaigona, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kauru a majalisar dokokin jihar Kaduna, ya gaza samar da ingantaccen wakilci tun bayan zaben sa.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai taken daga ‘Daga Fata zuwa Yaudara’ wanda kuma Junaidu Ishaq Maisalati, ya sanyawa hannu, kungiyar ta caccaki dan majalisar kan abin da ta bayyana a matsayin mai dimama kujera kuma ɗan siyasar da ya gaza wajen gudanar da ayukka a mazabar da kuma aikin da zai amfani al’umma.

Sanarwar ta koka da yadda al’ummar Kauru suka sanya kyakkyawan fata a shugabancin Danmaigona, amma a maimakon haka, ya kasa ba marada kunya.

Har ila yau, ta yi Allah-wadai da kawancen siyasarsa da Mukhtar Chawai, wani dan siyasa da aka ce ko ake zargin baya tabuka komai a mazabarsa ba, tare da bayyana cewa irin wannan kawancen yana kashe musu gwiwa matukar gaske.

KYA ta bayyana rashin jin dadin ta a kan abin da suka kira wasu ‘yan kudaden da basu gaza dubu 5 zuwa 10 da yake rabawa jama’a a matsayin yankawa kare ciyawa domin wannan ba abin da suke tsinanawa al’ummar da yake wakilta

Saboda haka Kungiyar ta bukaci al’ummar mazabar Kauru da su tashi tsaye akan nuna halin ko-in-kula a siyasance, su nemi wakilcin da ya dace, sannan su ki yarda a ba su kyauta irin wannan da bata tsinana musu komai.

Sun yi nuni da ‘yan majalisa irin su Hon. Shehu Yunusa na Kubau, wanda rahotanni suka ce ya ba da fifiko wajen hada kai da ci gaba, a matsayin misalan yadda wakilci na gaskiya ya kasance.

Da take kira da a wayar da kan ‘yan siyasa da kuma daukar matakin gama gari, sanarwar ta kalubalanci matasa da masu kada kuri’a a Kauru da su yi wa shugabanninsu hisabi, inda ta dage cewa zabe aiki ne..

KYA ta bayyana cewa Hon. Danmaigona ya samu damarsa, kuma har yanzu jama’a na nan suna jira, ba wai kawai alkawura ba, a’a, a samu canji na zahiri.

Rel/Yusuf Zubairu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’ar Bayero Ta Bayyana Alhininta Bisa Kisan Gillar Wani Dalibinta
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82