Sayar da Nunez zai ba Liverpool damar siyan Alexander Isak daga Newcastle.

Sai dai Newcastle ta ƙi karɓar tayin fam miliyan 110 daga Liverpool, saboda tana so ta siyar da Isak ne abkan fam miliyan 150.

Liverpool ta riga ta siyo Florian Wirtz daga Bayer Leverkusen a kan fam miliyan 116 da kuma Hugo Ekitike daga Frankfurt a kan fam miliyan 79.

Hakan ya sa Liverpool ta kashe kusan fam miliyan 250 a wannan kakar kasuwanni.

Ta kuma siyar da Luis Diaz ga Bayern Munich ankan fam miliyan 65.5 da Tyler Morton ga Lyon a kan fam miliyan 15.

Ɗan wasan Ingila Harvey Elliott ma na iya barin ƙungiyar a bana.

A watan Janairu da ya wuce, Liverpool ta ƙi karɓar tayin Yuro miliyan 70 daga Al-Nassr domin siyan Nunez.

A kakar da ta gabata, Nunez ya ci ƙwallaye bakwai ne kacal, amma a watan Yuli ya ci ƙwallaye uku cikin minti 20 a wasan da suka buga da Stoke City.

Al Hilal, wadda Simone Inzaghi ke jagoranta, ta zo ta biyu a gasar Saudi Pro League a bara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya fam miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami

Tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ba wa ɗalibar nan ’yar shekara 17 daga Jihar Yobe da ta lashe Gasar Turanci ta Duniya, Nafisa Abdullah Aminu, kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa ta OON.

Ya buƙaci a gayyato Nafisa da malamanta na harshen Turanci musamman zuwa Fadar Shugaban Ƙasa a karrama su saboda yadda suka ɗaga sunan Najeriya a idon duniya a fannin ilimi.

“Ina kira da babbar murya cewa a a ba wa Nafisa kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa daga Gwamnatin Tarayya.”

A cikin saƙon da ya wallafa a safiyar Talata, Pantami ya ƙara da cewa malaman Nafisa sun cancanci irin kyautar da aka yi wa tawagar masu horas da ’yan wasan Najeriya ta lambar OON da tsabar kuɗi Dala 50,0000 da kuma gida ga kowannensu, musamman ma tun da nasarar da suka samu a fannin ilimi ne.

’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje

“Su ma malananta a ba su kyauta irin wadda aka yi wa masu horas da ’yan wasan ƙwallon Najeriya. Wajibi ne mu ba wa ilimi muhimmancin da ya dace tare da karrama ƙwazon ’yan kasarmu,” in ji Pantami.

Bayanin na zuwa ne washegarin da Gwamnatin Tarayya ta yi irin wannan kyauta ga kowacce daga ’yan wasan ƙwallon kwandon Najeriya na D’Tigress kan lashe gasar Kaifin Nahiyar Afirka ta shekarar 2025.

Ƙasa da mako guda ke nan kuma bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi irin wannan kyauta ga ’yan wasan ƙwallon ƙafan mata ta Super Falcons bayan sun lashe gasar Kofin Nahiyar Afirka ta bana.

Aminiya ta ruwaito cewar Nafisa Abdullah Aminu ta lashe Gasar Turanci ta Duniya ta Teen Eagle da aka gudanar a ƙasar Birtaniya.

Nafisa daga Kwalejin Nigeria Tulip International (NTIC) da ke Jihar  Yobe ta doke abokan fafatawarta daga ƙasashe 69 domin zama Gwarzuwar Shekarar 2025.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti
  • An Biya Diyyar Naira Miliyan 277 Ga Wadanda Aikin Ginin Masallacin Gumel Ya Shafa
  • Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato
  • DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?
  • ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu
  • Nafisa ta cancanci kyautar Dala 100,000 da gida da OON — Pantami
  • FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
  • Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa