Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
Published: 7th, August 2025 GMT
Sayar da Nunez zai ba Liverpool damar siyan Alexander Isak daga Newcastle.
Sai dai Newcastle ta ƙi karɓar tayin fam miliyan 110 daga Liverpool, saboda tana so ta siyar da Isak ne abkan fam miliyan 150.
Liverpool ta riga ta siyo Florian Wirtz daga Bayer Leverkusen a kan fam miliyan 116 da kuma Hugo Ekitike daga Frankfurt a kan fam miliyan 79.
Hakan ya sa Liverpool ta kashe kusan fam miliyan 250 a wannan kakar kasuwanni.
Ta kuma siyar da Luis Diaz ga Bayern Munich ankan fam miliyan 65.5 da Tyler Morton ga Lyon a kan fam miliyan 15.
Ɗan wasan Ingila Harvey Elliott ma na iya barin ƙungiyar a bana.
A watan Janairu da ya wuce, Liverpool ta ƙi karɓar tayin Yuro miliyan 70 daga Al-Nassr domin siyan Nunez.
A kakar da ta gabata, Nunez ya ci ƙwallaye bakwai ne kacal, amma a watan Yuli ya ci ƙwallaye uku cikin minti 20 a wasan da suka buga da Stoke City.
Al Hilal, wadda Simone Inzaghi ke jagoranta, ta zo ta biyu a gasar Saudi Pro League a bara.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Saudiyya fam miliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
Yau 7 ga watan Nuwamba, Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar yin tazarce a wani sabon wa’adin shugabancin kasar Kamaru.
Shugaba Xi ya ce, kasar Sin da Kamaru suna da daddadiyar alaka mai kyau. A cikin ‘yan shekarun nan, amincewar siyasa tsakanin kasashen biyu ta kara zurfafawa, kuma an samu nasarori masu yawa a fannoni daban-daban na hadin gwiwa, tare da mara wa juna goyon baya a kan batutuwan da suka shafi muradunsu da kuma batutuwa masu muhimmanci.
A shekara mai zuwa ce za a cika shekaru 55 da kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasar Sin da Kamaru, matakin da ya samar musu da sabbin damammaki na ci gaban huldarsu. Xi yana dora muhimmanci sosai kan ci gaban dangantakar Sin da Kamaru, kuma yana fatan hadin gwiwa da shugaba Paul Biya, don aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Beijing a bara, ta yadda za a inganta cikakkiyar alaka ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare masu zurfi, da kyautata rayuwar al’ummomin kasashen biyu. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA