Sayar da Nunez zai ba Liverpool damar siyan Alexander Isak daga Newcastle.

Sai dai Newcastle ta ƙi karɓar tayin fam miliyan 110 daga Liverpool, saboda tana so ta siyar da Isak ne abkan fam miliyan 150.

Liverpool ta riga ta siyo Florian Wirtz daga Bayer Leverkusen a kan fam miliyan 116 da kuma Hugo Ekitike daga Frankfurt a kan fam miliyan 79.

Hakan ya sa Liverpool ta kashe kusan fam miliyan 250 a wannan kakar kasuwanni.

Ta kuma siyar da Luis Diaz ga Bayern Munich ankan fam miliyan 65.5 da Tyler Morton ga Lyon a kan fam miliyan 15.

Ɗan wasan Ingila Harvey Elliott ma na iya barin ƙungiyar a bana.

A watan Janairu da ya wuce, Liverpool ta ƙi karɓar tayin Yuro miliyan 70 daga Al-Nassr domin siyan Nunez.

A kakar da ta gabata, Nunez ya ci ƙwallaye bakwai ne kacal, amma a watan Yuli ya ci ƙwallaye uku cikin minti 20 a wasan da suka buga da Stoke City.

Al Hilal, wadda Simone Inzaghi ke jagoranta, ta zo ta biyu a gasar Saudi Pro League a bara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya fam miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama gungun wasu mutane da ake zargi da safarar mata zuwa kasar Saudiyya.

Hisbah ta dakile yunkurin mutanen ne a yayin da suke kokarin safarar wasu mata hudu daga jihohin Kano da Jigawa da Yobe, ta hannun wakilansu da ke sassan kasashen Yammacin Afirka?

Mataimakin Babban Kwamnand Hukumar, Dakta Mujahideen Aminudeen, ya ce masu safarar matan sun yaudarin matan da aka ceto cewa za su yi musu biza zuwa kasar Ghana inda daga nan za su wuce da su zuwa Saudiyya domin sama musu ayyukan yi.

An kana daya daga cikin mutanen ne a ranar Lahadi, wanda hakan ya kai ga cafke shugabansu da ake kira Bashir Sani Ibrahim.

Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025? Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Uku daga cikin matan masu shekaru 30 sn fito ne daga jihohin Kano da Jigawa a yayin da hudun mai shekara 35 da fito daga Jihar Yobe.

Dakta Aminudeen ya bayyana cewa matan sun biya mutanen Naira milian bibbyu, za su ciko Naira miliiyan 1.5 kowannensu domin sama musu biza.

Ya ce, “Wannan shi ne abin da muke ta gargadin mutane a kai — kar a yarda da tafiya ba tare da sanin inda za a kai su ba. Ana yaudarar mutane, ana kwace musu kuɗinsu, kuma da zarar sun isa ƙasashen waje ana tilasta musu shiga harkar karuwanci, fataucin miyagun ƙwayoyi ko kuma tsunduma cikin rayuwar kunci.”

Ya shawarci ’yan Najeriya da su guji irin waɗannan haɗurran tafiya, yana mai jaddada cewa kuɗin da ake ɓatawa wajen irin wannan safarar ya fi dacewa a saka shi a harkokin kasuwanci a gida.

“Da naira miliyan biyu ko uku da rabi, mutum zai iya fara kasuwanci mai kyau a Najeriya maimakon fadawa tarkon waɗannan miyagun dabaru,” in ji shi.

Ya nuna godiya cewa an samu damar dakile wannan yunkuri, yana mai cewa da masu safarar mutanen sun ci nasara, da lallai matan sun ɓace ba tare da sahu ba.

“Mun tattara bayanansu da fasfofonsu muka mika su ga Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane (NAPTIP). Za mu ci gaba da sa ido har sai an kammala bincike kan lamarin,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarihi da rayuwar Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh (1943-2025)
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 4,383, Sun Ceto 1,138 Daga Hannun Mahara Cikin Wata 3
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Kasar Sin Ta Mallaki Kusan Tashoshin Fasahar 5G Miliyan 4.65
  • DSS ta yi wa Malami tambayoyi kan harin da aka kai masa a Kebbi
  • Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC
  • Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja