Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II
Published: 7th, August 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya ce bai dace a riƙa bai wa mutanen da suka wawure dukiyar ƙasa manyan muƙaman gwamnati kamar ministoci ba.
A cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Sanusi II, ya bayyana damuwarsa game da yadda ’yan Najeriya ke son dukiya fiye da gaskiya da tarbiyya.
Ya ce al’umma na girmama masu kuɗi, ko da kuwa an san kuɗin haram ne.
“Ƙasar da ke bai wa mutanen da aka san sun wawure dukiyar ƙasa muƙamin minista, za ta ci gaba da tafiya a doro mara kyau,” in ji Sanusi.
“Ba ma jin kunya idan wani ɗan siyasa ya tara dukiya ta hanyar da ba ta dace ba, sai ma mu yi masa tafi.”
Sanusi ya ce mutane da dama yanzu na shiga siyasa ne don su tara kuɗi, ba don su yi wa jama’a aiki ba.
Ya ƙara da cewa irin waɗannan shugabanni suna auna darajarsu ne da adadin gidajen da suke da su, jiragen sama masu zaman kansu, ko kuɗaɗe a asusun banki.
Ya ce ba su damu da irin kyakkyawan tasirin da suka yi wa al’umma ba.
Ya kuma ce rashin tarbiyya da gaskiya a tsakanin shugabanni na ƙara raunana tsarin gwamnati gaba ɗaya.
A cewarsa, wasu ba su damu da abin da mutane za su ce game da su ba muddin sun mallaki dukiya.
Yayin da yake tunawa da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Murtala Muhammed, Sanusi ya ce Najeriya na buƙatar dawo da kyawawan ɗabi’u irin na shugabannin da suka gabace mu.
“Muna buƙatar daidaita ɗabi’unmu gaba ɗaya,” in ji shi.
“Ba wai shugaban ƙasa ko gwamnoni kaɗai ba ne za su canja ƙasa, kowa na da rawar da zai taka.”
Ya ƙara da cewa ’yan siyasa sun lalata tsarin aikin gwamnati, kuma Najeriya na buƙatar gina tsari mai ƙarfi da zai bai wa ma’aikatan gwamnati damar ƙin amincewa idan suka nemi su karya doka.
Sanusi, ya jaddada cewa kamata ya yi al’ummar Najeriya ta bai wa ɗabi’u kamar gaskiya, aiki tuƙuru, da tausayawa fifiko sama da tara dukiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan siyasa Ɓarayi Rashin Gaskiya Sarki Sanusi II
এছাড়াও পড়ুন:
APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
“A wani ɓangare na wannan dubarar, jam’iyyar a ƙarƙashin kulawar ɗaya daga cikin manyan ma’aikatan gwamnati, ta yi ƙoƙarin shirya zaɓen jagoranci ƙungiyar Musulmai ƴ an asalin Jihar Filato a cibiyar Azi Nyako da ke Dadin-Kowa a garin Jos, wanda daga bayanan da aka samu lamarin ya kasa samun nasara.
“PDP na ganin cewa da wannan dubarar na raba kan Musulmin Jihar Filato za ta iya samun nasara a zaɓen 2027, wanda wannan ka iya kawo rashin jituwa da haɗin kan al’umma, musamman a irin wannan lokaci da ake fama da rikice-rikice addini da ƙabilanci da kuma ayyukan ƴ an ta’adda, wanda hakan bai kamata a siyasantar da addini ba.
“Yadda PDP ke amfani da addini a matsayin hanyar lashe zaɓe, tana sake dawo da amfani da siyasa mara tsafta wajen lashe zaɓen 2027 da kowacce hanya,” in ji mai magana da yawun APC.
Amma shugaban PDP na yankin tsakiyar Nijeriya, Monday Daspan, ya musanta wannan zargin a matsayin wanda ba shi da tushe ballantana makama.
“Bamaiyi ya shigo harkar siyasa ta bayan fage ba hanyar da ya kamata ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa hakan ya yi masa sauƙi wajen gwama addini da harkokin siyasa. Mafi yawan waɗanda suka shigo harkar siyasa ta bayan fage ba su da cikakken ƙwarewa wajen yin magana a cikin harkokin siyasar ƙasar nan.
“Mu a matsayinmu, APC ba za su iya daidaita tsakanin mulki da ci gaba ba. Sun yi rashin nasara kan zaɓe kuma suna son danganta shi da wani abu. Matsalar a nan dai ita ce, Gwamna Celeb Mutfwang yana aiki ko kuma ba ya yi? Eh. Shin Lalong ya yi aiki da ya yi? A’a,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp