Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin minista ba — Sarki Sanusi II
Published: 7th, August 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya ce bai dace a riƙa bai wa mutanen da suka wawure dukiyar ƙasa manyan muƙaman gwamnati kamar ministoci ba.
A cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Sanusi II, ya bayyana damuwarsa game da yadda ’yan Najeriya ke son dukiya fiye da gaskiya da tarbiyya.
Ya ce al’umma na girmama masu kuɗi, ko da kuwa an san kuɗin haram ne.
“Ƙasar da ke bai wa mutanen da aka san sun wawure dukiyar ƙasa muƙamin minista, za ta ci gaba da tafiya a doro mara kyau,” in ji Sanusi.
“Ba ma jin kunya idan wani ɗan siyasa ya tara dukiya ta hanyar da ba ta dace ba, sai ma mu yi masa tafi.”
Sanusi ya ce mutane da dama yanzu na shiga siyasa ne don su tara kuɗi, ba don su yi wa jama’a aiki ba.
Ya ƙara da cewa irin waɗannan shugabanni suna auna darajarsu ne da adadin gidajen da suke da su, jiragen sama masu zaman kansu, ko kuɗaɗe a asusun banki.
Ya ce ba su damu da irin kyakkyawan tasirin da suka yi wa al’umma ba.
Ya kuma ce rashin tarbiyya da gaskiya a tsakanin shugabanni na ƙara raunana tsarin gwamnati gaba ɗaya.
A cewarsa, wasu ba su damu da abin da mutane za su ce game da su ba muddin sun mallaki dukiya.
Yayin da yake tunawa da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Murtala Muhammed, Sanusi ya ce Najeriya na buƙatar dawo da kyawawan ɗabi’u irin na shugabannin da suka gabace mu.
“Muna buƙatar daidaita ɗabi’unmu gaba ɗaya,” in ji shi.
“Ba wai shugaban ƙasa ko gwamnoni kaɗai ba ne za su canja ƙasa, kowa na da rawar da zai taka.”
Ya ƙara da cewa ’yan siyasa sun lalata tsarin aikin gwamnati, kuma Najeriya na buƙatar gina tsari mai ƙarfi da zai bai wa ma’aikatan gwamnati damar ƙin amincewa idan suka nemi su karya doka.
Sanusi, ya jaddada cewa kamata ya yi al’ummar Najeriya ta bai wa ɗabi’u kamar gaskiya, aiki tuƙuru, da tausayawa fifiko sama da tara dukiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan siyasa Ɓarayi Rashin Gaskiya Sarki Sanusi II
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Zaman Lafiya ta Duniya: Kungiyar Arewa Ta Nemi Ƙarfafa Sirrin Tsaro Don Kare ‘Yan Najeriya
A yayin da ake gudanar da shagulgulan ranar zaman lafiya ta Duniya ta Bana, Kungiyar rajin tabbatar da zaman lafiya da hadin Kai da kuma cigaban Arewacin Nigeria ta yi Kira ga Gwamnati a dukkan matakai da kuma Hukumomin tsaro su karfafa amfani da bayanan tsaro na sirri wajen kare rayukan al’ummar Kasa.
Shugaban Kungiyar ta ACI Dakta Abdullahi Idris ya yi wannan Kira a wani taron manema labarai da Kungiyar ta Kira a Kaduna.
Ya yi bayanin, Kungiyar ta lura da matakan da Gwamnati da Hukumomin tsaro suka dauka domin maido da zaman lafiya a wasu sassan Arewcin Kasar nan.
Dakta Abdullahi Idris ya ce, matakan da aka dauka abin a yaba ne, Amma kuma sun yi kadan matuka wajen magance matsalalon tsaro da suka addabi Kasar nan.
Ya jadda da bukatar ganin Shugabanni da masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro su daina nuna son zuciya da siyasantar da sha’anin tsaron Kasa domin amfanin al’umma.
Dakta Abdullahi Idris ya tunatar da Shugabanni cewa Allah zai tambaye su yadda suka Shugabanci al’umma, a ranar gobe kimyama.
Daga nan sai Shugaban Kungiyar ya bukaci Gwamnati a dukkan matakai da Hukumomin tsaro su rubunya kokarin da suke yi kana su yi amfani da rahitannin tsaro na sirri wajen maganin wannan matsala ta tsaro.
COV/LERE