Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
Published: 14th, April 2025 GMT
Kasurgumin dan ta’addar nan da ke addabar yankin Sakkwato ta Gabas da Zamfara, Kacalla Bello Turji ya kashe manoma 11 a garin Lugu cikin Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.
Dan gwagwarmaya da ke biye da lamarin rashin tsaro a yankin Sakkwato ta Gabas Bashiru Altine Guyawa ya sanar wa manema labarai cewa, Turji ya dawo daga yawon sallah ne ya far wa garin da hari.
“Turji da yaransa sun bar kauyensa na Fakai a Karamar Hukumar Shinkafi suka shiga wasu kauyukka a Karamar Hukumar Isa a hanyarsu ta komawa Fakai bayan sun gama yawon Sallah suka kashe manoma 11.”
Guyawa yana ganin laifin jami’an tsaro kan lamari, inda suka gaza daukar mataki kan bayanan sirri da suke da shi.
Dan majalisar dokokin jiha, Honarabul Aminu Boza ya ce, ya samu bayanin sai dai dan bindigar bai shiga yankin da yake wakilta ba a lokacin bikin Sallah.
Ya ce, “muna sane da cewa Turji ya shirya kai ziyara a gabashin Gatawa, a nan ne muka dauki mataki, mun je Sabon Birni, inda muka dauki matakin tsaro don kare faruwar hakan, shi ne dalilin huce haushinsa a kan manoma a Isa’’.
Akwai bayanan da ke nuna cewa, Turji ya tsaya a kauyen Tozai, ya kashe shugaban ‘yan sintiri na garin.
A lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Ahmad Rufa’i ya ce, jami’an soja ne kadai za su iya tabbatar da farmakin saboda su ne ke aiki a yankin.
Duk da sojoji sun ayyana suna neman Turji ruwa jallo, amma ya ci gaba da kai farmaki a kauyukkan gabashin Sakkwato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF), ta ce ta taka muhimmiyar rawa wajen daƙile yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin, bayan wasu sojoji sun bayyana hamɓarar da Gwamnatin Shugaba Patrice Talon.
Gungun sojojin, sun bayyana cewa ta rushe gwamnati tare da dakatar da kundin tsarin mulki, da rufe iyakokin ƙasar.
An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a KanoSun kuma ayyana Laftanar Kanar Tigri Pascal a matsayin Shugaban gwamnatin soja.
Daga baya gwamnatin Benin ta sanar da cewa sojojin ba su yi nasarar yin juyin mulkin ba.
Rahotanni sun nuna cewa jiragen yaƙin Najeriya sun shiga ƙasar domin kare dimokuraɗiyya, duk da cewa babu cikakkun bayanai ba.
NAF, ta tabbatar da cewa ta yi aiki a Benin bisa yarjejeniyar tsaro ta ECOWAS.
“Sojojin Saman Najeriya sun yi aiki a Jamhuriyar Benin bisa ƙa’idojin ECOWAS da umarnin Rundunar Tsaro ta Yanki,” in ji Air Commodore Ehimen Ejodame.
ECOWAS, ta yi Allah-wadai da yunƙurin juyin mulkin, tare da cewa za ta kare dimokuraɗiyyar ƙasar idan buƙatar hakan ta taso.
“ECOWAS za ta tallafa wa gwamnati da al’ummar Benin, har da tura rundunar tsaro ta yankin, domin kare kundin tsarin mulki da ikon ƙasar,” in ji sanarwar ECOWAS.