Aminiya:
2025-07-11@07:18:36 GMT

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasurgumin dan ta’addar nan da ke addabar yankin Sakkwato ta Gabas da Zamfara, Kacalla Bello Turji ya kashe manoma 11 a garin Lugu cikin Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

Dan gwagwarmaya da ke biye da lamarin rashin tsaro a yankin Sakkwato ta Gabas Bashiru Altine Guyawa ya sanar wa manema labarai cewa, Turji ya dawo daga yawon sallah ne ya far wa garin da hari.

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

“Turji da yaransa sun bar kauyensa na Fakai a Karamar Hukumar Shinkafi suka shiga wasu kauyukka a Karamar Hukumar Isa a hanyarsu ta komawa Fakai bayan sun gama yawon Sallah suka kashe manoma 11.”

Guyawa yana ganin laifin jami’an tsaro kan lamari, inda suka gaza daukar mataki kan bayanan sirri da suke da shi.

Dan majalisar dokokin jiha, Honarabul Aminu Boza ya ce, ya samu bayanin sai dai dan bindigar bai shiga yankin da yake wakilta ba a lokacin bikin Sallah.

Ya ce, “muna sane da cewa Turji ya shirya kai ziyara a gabashin Gatawa, a nan ne muka dauki mataki, mun je Sabon Birni, inda muka dauki matakin tsaro don kare faruwar hakan, shi ne dalilin huce haushinsa a kan manoma a Isa’’.

Akwai bayanan da ke nuna cewa, Turji ya tsaya a kauyen Tozai, ya kashe shugaban ‘yan sintiri na garin.

A lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Ahmad Rufa’i ya ce, jami’an soja ne kadai za su iya tabbatar da farmakin saboda su ne ke aiki a yankin.

Duk da sojoji sun ayyana suna neman Turji ruwa jallo, amma ya ci gaba da kai farmaki a kauyukkan gabashin Sakkwato.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar EFCC Ta Kai Wa Yaran Makaranta Yaki Da Rashawa A Ilorin

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC shiyyar Ilorin ta kai wa daliban makaranta yakin da ta yi da cin hanci da rashawa domin fadakar da su illar cin hanci da rashawa.

 

Da yake jawabi ga dalibai a makarantar Nursery da Primary School, Tanke, Ilorin, Shugaban Sashen Hulda da Jama’a, Daraktan Hukumar EFCC, Ayodele Babatunde, ya ilmantar da daliban a kan ma’anar cin hanci da rashawa, daban-daban da illolinsa da yadda kowa da kowa, ciki har da yara, za su iya bayar da tasu gudunmuwar wajen gina Nijeriya mara cin hanci da rashawa.

 

Ya ce cin hanci da rashawa yana yin abin da bai dace ba ne, musamman idan ya shafi wasu ko kasar da suka hada da munanan dabi’u kamar ha’inci da karya da kuma sata.

 

Babatunde ya ce yara suna da rawar da za su taka wajen samar da makoma mai kyau ko da a kanana.

 

“Za ku iya kauce wa cin hanci da rashawa ta hanyar fadin gaskiya a kodayaushe, yin aikin gida ba tare da yin kwafin wasu ba, kin yin sata ko zamba, kiyaye gaskiya, da’a, amana, da kishin kasa da mutunta doka a gida da makaranta,” inji shi.

 

Babatunde ya kara karfafa gwiwar daliban da su tabbatar sun girma a matsayin ’yan kasa nagari masu kaunar kasarsu tare da yin watsi da ayyukan da ka iya cutar da ci gabanta.

 

Tattaunawar ta kunshi tambayoyi daga daliban da kuma alkawarin zama jakadun yaki da cin hanci da rashawa a makarantarsu da gidajensu.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU/Ilorin

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
  • Hukumar EFCC Ta Kai Wa Yaran Makaranta Yaki Da Rashawa A Ilorin
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi