Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran
Published: 14th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana alhininsa akan rasuwar Dr. Akbar I’itimadi wanda shi ne na farko da ya kafa hukumar makamashin Nukiliya ta Iran.
Wasikar ta’aziyyar da shugaban kasa ta kunsa ta ambaci cewa: Shakka babu hidima mai kima da wannan masanin ya yi, ya share fagen gina da ci gaban fasahar makamashin Nukiliya a Iran da kuma mayar da kasar mai cin gashin kanta a wannan fage.
Har ila yau, shugaban kasar ta Iran ya mika sakon ta’aziyyarsa ga masana na Iran, da kuma iyalansa. Ya kuma yi addu’a da rokon Allah madaukin sarki da ya lullube shi da rahamarsa da kuma gafararsa, sannan ya bai wa iyalansa na hakuri.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja, ya yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan kama Abubakar Abba, jagoran kungiyar Mahmuda, daya daga cikin manyan kungiyoyin ta’addanci da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi a Najeriya.
An ce an kama shi ne a Wawa da ke karamar hukumar Borgu ta Jihar Neja inda aka kai shi Abuja domin ci gaba da bincike.
Gwamna Umar Bago ya bayyana matakin a matsayin nuni da irin jajircewar da shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi na tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan Nijeriya.
Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin babban sakataren yada labaran sa, Bologi Ibrahim, ya ce, “Eh gaskiya ne, zan iya tabbatar da cewa hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban kungiyar Mahmuda da ke daya daga cikin kungiyoyin ta’addanci a yammacin Afirka, Abubakar Abba, wanda jami’an tsaron farin kaya DSS suka kama shi da ransa.
“Wannan babbar nasara ce a gare mu a matsayinmu na jama’a da kuma gwamnati, kuma Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan labari mai ban sha’awa, yana mai jaddada cewa “Kamun Abba ya nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen kawo karshen rashin tsaro da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya. In ji Gwamna Bago.
Gwamnan ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar Neja za ta ci gaba da hada kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin ganin an dakile ta’addanci a jihar Neja da Najeriya.
ALIYU LAWAL.