Aminiya:
2025-11-25@05:01:44 GMT

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

Published: 14th, April 2025 GMT

Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.

Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.

A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.

Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.

Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

A sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.

Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”

Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, ta daƙile wani hari da ’yan bindiga suka kai wa al’ummar Kuraje da ke gefen birnin Gusau.

Wasu gungun ’yan bindiga, ɗauke da makamai ne, suka kutsa cikin ƙauyen suna harbi, lamarin da ya jefa mazauna Kuraje da maƙotan ƙauyukan cikin tashin hankali.

Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja

A yayin harin, sun yi awon gaba da mata 10 da yara 15.

Kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya ce ’yan sanda sun ɗauki mataki bayan samun kiran gaggawa.

Ya ce tawagar haɗin gwiwa daga sashen Damba, Sashen Ayyuka da kuma Rundunar Tsaron Al’umma (CPG) sun isa ƙauyen cikin gaggawa.

Sun bi sahun ’yan bindigar, sannan suka yi artabu da su.

’Yan sanda sun ceto dukkanin mutum 25 ba tare da kowa ya ji rauni ba.

An kai matan da yaran zuwa Sabon Gari Damba domin kula da su, kafin su da iyalansu.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya yaba wa jarumtar jami’an da suka yi aikin, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 5 a Kudancin Beirut
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
  • Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu
  • Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Bukaci shugaba Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno