Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
Published: 14th, April 2025 GMT
Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.
Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.
A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.
Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.
Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoA sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.
Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”
Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum 25 kan zargin shirya auren jinsi a Kano
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta samu nasarar cafke wasu mutum 25 da ake zargi da shirya auren jinsi a samamen da ta kai wani wurin shagali a jihar.
A cewar hukumar, an kama mutanen ne da yammacin Asabar a wani wurin taro da ke kan titin Hotoro Bypass a ƙaramar hukumar Tarauni.
Sojoji sun daƙile harin ISWAP a Borno NSCDC ta yi alhinin mutuwar Kwamishinan Tsaron GombeMataimakin Kwamanda Janar na Hukumar Hisbah mai kula da ayyuka na musamman, Sheikh Dokta Mujahid Aminuddeen Abubakar, ne ya tabbatar da kama waɗanda ake zargin a ranar Lahadi.
Ya bayyana cewa samamen na zuwa ne bayan bayanan sirri da hukumar ta samu daga wani mai kishin al’umma.
Ya bayyana cewa bayanan sirrin sun nuna cewa wani mai suna Abubakar Idris yana shirin auren wani matashi, lamarin da ya sa jami’an Hisbah suka bazama zuwa wurin da taron ke gudana.
Ya ƙara da cewa daga cikin wadanda aka kama akwai maza 18 da aka bayyana a matsayin ’yan daudu, da kuma mata 7 daga unguwanni daban-daban ciki har da Sheka, Yar Gaya da Kofar Nasarawa.
Dokta Mujahid ya ce a halin yanzu duk ababen zargin suna hannun hukumar, kuma za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Ya yi kira ga iyaye da su kula wajen inganta tarbiyyar ’ya’yansu, tare da roƙon jama’a da su rika sanar da hukumar Hisbah ko hukumomin tsaro idan sun ga wani abin da ke da ɗaukar hankali.
Mataimakin kwamandan ya sake jaddada ƙudirin hukumar na ci gaba da tabbatar da ɗabi’a ta gari da kare mutuncin Kano a matsayin jihar da aka sani kan ginshiƙin ladabi da ƙa’idojin addinin Musulunci.