Aminiya:
2025-11-26@19:27:28 GMT

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

Published: 14th, April 2025 GMT

Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.

Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.

A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.

Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.

Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

A sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.

Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”

Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

Yundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta tabbatar da cewa ɗaya daga cikin ’yan mata 14 da ƙungiyar ISWAP ta sace a Ƙaramar Hukumar Askira-Uba ta kuɓuta, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano sauran 13.

A sanarwar da ya fitar dangane da irin ƙoƙarin da Jami’an tsaron ke yi na ceto sauran ‘yan matan 13 da ke hannun ‘yan ta’addan, kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce, shugaban gundumar Huyum ya bayar da rahoto a ranar Asabar 22 ga Nuwamba cewa waxanda ake zargin mayaƙan Ƙungiyar ISWAP ne suka sace ‘yan matan, yayin da suke aiki a wata gona a gundumar Mussa.

Tawagar ’yan sanda, sojoji, Sibiliyan JTF, da mafarauta da ’yan banga nan da nan suka fara aikin bincike don ceto ’yan matan.

“Ɗaya daga cikin waxanda abin ya shafa ta tsira ba tare da wata matsala ba a lokacin aikin kuma an ceto ta,” in ji Daso.

Mayaƙan Boko Haram sun file kan mata 2 a Borno Sace ɗalibai: Idan ba zai iya ba ya sauka kawai— PDP

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Naziru Abdulmajid, ya yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu lura yayin da hukumomin tsaro ke ƙara himma wajen ƙoƙarin ceto sauran ‘yan matan.

Sanarwar ta ce, “Ana shawartar manoma da mazauna yankin da su yi aiki a yankunan da jami’an tsaro ke sintiri,” in ji sanarwar.

Rundunar ta ce za a samar da ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da aikin gano wurin da waɗannan mata suke.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi