Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
Published: 14th, April 2025 GMT
Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.
Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.
A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.
Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.
Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoA sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.
Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”
Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
Babban Bankin Najeriya (CBN) ya soke iyakance adadin kuɗin da mutum ko kamfani za su iya ajiyewa a banki sannan ya ƙara yawan kudin da za a iya fitarwa a mako da ₦100,000 zuwa ₦500,000.
Wannan na cikin wata sanarwa da Daraktar Sashen Tsarin Kuɗi da Dokoki ta bankin, Dr. Rita Sike, ta sanya wa hannu kuma ta fitar ranar Laraba.
Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohiA cewar bankin, an yi sauye-sauyen manufofin ne da nufin rage tsadar sarrafa kuɗi, magance matsalolin tsaro, da kuma dakile haɗarin safarar kuɗi ba bisa ka’ida ba da ke da alaƙa da dogaro da mu’amalar kuɗi kai tsaye.
CBN ya ce manufofin da suka gabata kan kuɗi an gabatar da su ne domin rage amfani da kuɗi kai tsaye da ƙarfafa amfani da hanyoyin biyan kuɗi ta intanet.
Sai dai, sauye-sauyen tattalin arziki da na gudanarwa sun sa dole a sake duba dokokin domin daidaita su da halin da ake ciki a yanzu.
Daga ranar 1 ga watan Janairun 2026, an soke iyakance adadin kuɗin da za a iya ajiye gaba ɗaya, kuma ba za a sake cajin kuɗin da ake ɗauka a kan ajiya mai yawa ba.
Sabbin dokokin sun jingine iyakance fitar kuɗi na mako gaba ɗaya ga mutum ɗaya zuwa ₦500,000, yayin da na kamfanoni ya koma ₦5m.
Kazalika, dokar ta ce fitar kuɗin da ya wuce waɗannan iyakokin zai jawo ƙarin caji na kaso cikin 100 ga mutum ɗaya da kuma kaso biyar cikin 100 ga kamfanoni, inda za a raba kuɗin da aka tara da bankuna bisa tsarin 40:60 tsakanin CBN da bankunan da abin ya shafa.
CBN ya kuma umarci bankuna da su tabbatar da cewa sun saka dukkan nau’o’in kuɗi a cikin na’urar ATM domin sauƙaƙa samun kuɗi.
Babban bankin ya kuma umarci bankuna da su rika gabatar da rahoton wata-wata ga Sashen Kula da Bankuna, Sashen Kula da Sauran Hukumomin Kuɗi, da Sashen Kula da Tsarin Biyan Kuɗi domin tabbatar da bin doka.