Aminiya:
2025-12-04@08:59:44 GMT

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

Published: 14th, April 2025 GMT

Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.

Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.

A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.

Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.

Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

A sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.

Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”

Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja

Wata gobara ta tashi a ranar Laraba ta ƙone kasuwar katako da ke kusa da Jabi Masallaci a Abuja.

Gobarar ta lalata kaya da kayan gini na miliyoyin kuɗi, amma ba a yi asarar rai ba.

CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000 Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina

Kawo yanzu dak ba a san musababbin tashin gobarar ba.

Sai dai wasu rahotanni na cewa gobarar na iya farawa ne sakamakon matsalar wutar lantarki, wanda wani lokacin wayoyin wuta na faɗowa kan rumfunan kasuwa.

’Yan kasuwa da mazauna yankin sun yi ƙoƙarin kashe wutar, amma ta yaɗo cikin sauri saboda katako da sauran kayayyakin gini na da saurin kamawa da wuta.

Wasu gine-gine da ke kusa da kasuwar sun lalace, lamarin da ya tilasta wa jama’a gudu domin tsira da rayukansu.

Daga baya jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya sun isa wajen tare da kashe wutar.

Mutanen da abin ya shafa sun roƙi gwamnati ta taimaka musu, domin sun rasa duk abin da suka dogaro da shi wajen kula da rayuwarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus