Babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa na yankin tekun Farisa (PGCC) ya yi fatan alkhairi ga kasashen Iran da Amurka a tattaunawa ba kai tsaye ba a tsakaninsu dangane da shirin Nukliya ta kasar Iran na zaman lafiya wanda suka fara, a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jasem Mohamed AlBudaiw yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa, kungiyar tana bukatar gidan an warware matsaloli tsakanin kasashen duniya ta hanyar tattanawa.

  Haka ma tsakanin kasashen yankin.

AlBudaiw ya yabawa kasar Omman da shirya wannan tattaunawar, sannan ya yi fatan tattaunawan da aka fara zai kai ga rage tada jijiyoyin wuya a yankin da kuma kasashen duniya, ya kuma ce kasashen yankin suna fatan zasu kai ga sakamako mai kyau tsakanin kasashen biyu.

Gwamnatin kasar Iran dai tana har yanzun suna shakkar kasar Amurka saboda yawan yaudarar da tayiwa kasar a baya. Musamman fitar kasar daga yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2018. Da kuma yawan takunkuman da ta dorawa a kasar tun lokacin.

Daga karshe babban sakataren kungiyar ta PGCC ya ce tana fatan za’a kawo karshen duk wani rikici a gabas ta tsakiya daga ciki har da na HKI a falasdinawa a Gaza ta hanyar tattaunawa da fahintar Juna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta amince da wasu sauye-sauye da nufin rage tsadar tafiye-tafiyen jiragen sama a tsakanin kasashe mambobin kungiyar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, Hukumar ECOWAS ta sanar da cewa shugabannin kasashe da gwamnatoci, a taronsu a Abuja, sun amince da wata manufa ta kawar da harajin sufurin jiragen sama da kuma rage kudin tikitan jirgin sama da kashi 25 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

Hukumar ta bayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan shekaru da dama na koma baya a fannin sufurin jiragen sama a Yammacin Afirka, galibi saboda yawan haraji, wanda ke hana bukatar tafiye-tafiye da kuma raunana jarin da ake zubawa a fannin tafiye tafiye na jiragen sama.

Nazarin da ECOWAS da Tarayyar Afirka, da Kungiyar Jiragen Sama ta Afirka (AFRAA), da Kungiyar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (IATA) suka gudanar sun nuna cewa Yammacin Afirka ya kasance daya daga cikin yankuna mafi tsada don tafiye-tafiyen jiragen sama, inda fasinjoji wani lokacin ke biyan har zuwa caji 66 daban-daban, yayin da kamfanonin jiragen sama ke fuskantar kudade daban-daban.

ECOWAS ta yi gargadin cewa hauhawar farashin jiragen sama na hana tafiye-tafiyen fasinjoji, rage yawan yawon bude ido, kawo cikas ga ciniki, da kuma lalata ajandarta ta ‘yancin zirga-zirga da hadewar yankuna.

A cewar sanarwar, amincewa da Dokar na da nufin magance wadannan kalubalen da kuma daidaita yankin da ka’idojin jiragen sama na duniya.

Kungiyar ta jaddada cewa ya kamata wadannan gyare-gyare su taimaka wajen rage farashin tikiti, kara yawan fasinjoji, karfafa kamfanonin jiragen sama na yankin, bunkasa ayyukan filayen jiragen sama da kuma samar da karin damammaki na tattalin arziki ga al’ummomin da ke karbar bakuncin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  
  • Hamsa: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjeniyar Tsagaita Bude Wuta A Yankin
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim