Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:13:52 GMT

Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Published: 22nd, March 2025 GMT

Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Bubu da kari, abin mahimmancin shi ne, shi talakan Nijeriya zai iya gani a kas na irin wadannan shirye-shiyen da gwamnatin ke son aiwatarwa?

 

Fannin Da Gwamnatin Za Ta Zuba Kudaden:

A kasafin kudin na 2025, Gwamnatin Tarayya ta warewa bangaren tsaro Naira tiriliyan 6.11 wanda ya kai ta samar da karin kaso 88 daga cikin kasafin kudin da ta warewa fannin na Naira tiriliyan 3.

25 a 2024.

Shin wannan burin na Gwamnatin zai iya cika, duba da yadda aka gaza dakile ta’addanci, ‘yan fashin daji, wanda idan ba a mayar da hankali ba, a 2025, tarihi ne zai sake mai-maita kansa.

An ware Naira tiriliyan 5.99 a cikin kasafin kudin don yin tituna, gadoji da kuma manyan ayyuka a babbar hanyar da ta tashi daga Legas zuwa Kalaba da ta Sokoto zuwa Badagry, inda aka samu karin da ya kai sama da kaso 350 sabanin Naira tirliyan 1.32 da aka ware a kasafin kudin bara.

Idan har da a gudanar da wadannan ayyukan, za su kara samar da ayyukan yi da habaka kasuwanci.

Bugu da kari, a kasafin kudin na 2025, an warewa ilimi, kiwon lafiya da bunkasa hazaka Naira biliyan 5.7 wanda ya kai kaso 161, sabanin Naira tiriliyan 2.18 da aka ware a kasafin kudi na 2024, inda fannin aikin noma ya samu Naira tiriliayan 3.73, wanda hakan ya nuna an samu kari mai yawa da ya zarta na Naira biliyan 362, inda an yin wannan karin ne, don a karya farashin kayan abinci a kasar.

 

Sai dai, shin ko wannan karin kudaden zai samar wa talakawan kasar sauki?

Amma wasu kwararu a Cibiyar Tsare-Tsare Da Bincike Kan Tattalin Arzikin Kasa (CEPR) ta yi nuni da cewa, idan har ba a wanzar da kuma kara kudi a cikin kasafin kudi hakan ba zai yi tasiri ba.

 

Kara Yawan Karbo Rancen Kudade:

Kudin ruwan da bashin da Gwamnatin ke biya ya lakume Naira tirilaya 16.3, wanda ya kai kaso 98, inda hakan ya nuna an samu karin Naira 8.25 a kasafin kudi na 2024.

Sai dai, wani babban kalubalen shi ne, yadda Nijeriya ke biyan bashin kudin ruwa na bashin da ta karbo fiye da wanda rake son kashewa a bangarorin ilimi, kiwon lafiya da samar da kayan aiki.

Gwamnatin ta yi hasahsne kudaden shiga da take son samu za su karu daga Naira tiriliyan18.32 zuwa Naira 36.35 trillion, wadanda suka kai karin kaso 123.19, musamman ta hayar tara haraji da zuba hannun jari na ketare.

Duba da yadda a arihin Nijeriya ka gaza tara kudaden shigar da ake sa ran tarawa, wasu kwararru a taron kungiyar tattalin arziki Nijeriya (NESG) sun yi garadin cewa, bai mai yuwa banen wadannan hasashen da aka yi su tabbata ba.

Kasafin kudin kasar ya rubanya a cikin shekara daya, amma duk da haka kudaden shigar kasar sun yi rauni.

Alal misali, a cikin kasafin kudin na 2025, ‘yan Majalisa sun samu karin Naira biliyan 344.85, wanda a kasafin kudi na 2024, suka samu karin Naira biliyan 197.93, inda kuma su ke son ‘yan kasar su kara jan damarar ci gaba da kula da rayuwarsu.

Bugu da kari, ‘yan Malasira Dokoki sun sun samawar da kansu karin sma da Naira biliyan 7 na kudaden sun a tafiye-tafiye, da kuma wasu dimbin kudaden da suka warewa kansu na jin dadi da na biyan kafafen ‘yada labarai.

A shirye-shiyen jin kan alumma, an ware Naira biliyan 723.68 kacal wanda aka kara kudin zuwa Naira biliyan 600, amma duk da haka, wani dan bangare kadan ne, aka kashe kan ayyukan gwamnatin.

Akwai dai dimbin buri da aka sanya a cikin kasafin kudin na 2025, wanda duk da wannan burin, cin abinci sauku a rana, na neman gagarar talakan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Naira tiriliyan Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027

’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.

Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Duk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).

Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.

Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.

“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.

Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.

Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.

“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.

Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.

A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.

Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.

Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.

“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.

Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?

Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.

“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.

“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.

Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.

Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.

Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.

Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.

Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.

“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi