MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
Published: 29th, March 2025 GMT
Babban sakataren MDD, Antonio Guterres ya yi gargadi a jiya juma’a da safe, akan abinda ya kira ‘yanayi mai cike da damuwa da yake faruwa a cikin kasar Sudan ta Kudu.
An sami tashin hankali da fadace-fadace a cikin kasar ta Sudan ta kudu a ranar Laraba da jami’an tsaro su ka yi wa mataimakin shugaban kasa na farko Riek Machar daurin talala a cikin gidansa.
Babban magatakardar MDD ya yi kira ga ‘yan siyasar kasar ta Sudan ta Kudu da su ci gaba da riko da yarjejeniyar sulhu da zaman lafiya,inda ya ce: “ A dawo da gwamnatin hadin kan kasa, da aiki da alkawullan da aka yin a zaman lafiya da sulhu, da hakan ne kadai hanyar dawo da zaman lafiya da kuma yin zabe a cikin watan Disamba 2026.”
A halin da ake ciki a yanzu, kungiyar tarayyar Afirka tana aikin hadin gwiwa da MDD domin kawo karshen dambaruwar siyasar da ake ciki a kasar.”
Gutrres ya ce; Muna goyon bayan tarayyar Afirka na aikewa da tawagar dattijan nahiyar zuwa Afirka ta kudu da kuma wata tawagar a karkashin jagorancin shugaban kasar Kenya Ruto.
Babban sakataren MDD ya kira yi shugabannin kasar ta Sudan Ta Kudu das u ajiye makamansu na yaki, su kuma bai wa al’ummar kasar fifiko.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
A nata bangare kuwa, Amurka ta bayyana aniyarta ta aiki tare da bangaren Sin, wajen ci gaba da warware sabani a fannonin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar tsarin gudanar da shawarwari, da ingiza damar samar da karin nasarori daga tattaunawar, da kara samar da daidaito a alakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Wakilin cinikayya na kasa da kasa na Sin karkashin ma’aikatar cinikayya, kuma mataimakin ministan cinikayyar kasar Li Chenggang, ya bayyana a yayin da yake yiwa manema labarai karin haske game da zaman tattaunawar sassan biyu. Ya ce sassan biyu suna sane da muhimmancin wanzar da daidaito, da kyautata alakar tattalin arziki mai nagarta tsakanin Sin da Amurka, sun kuma yi kyakkyawar musaya game da muhimman batutuwan cinikayya da na raya tattalin arziki dake jan hakulansu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp