HausaTv:
2025-05-01@00:44:22 GMT

MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu

Published: 29th, March 2025 GMT

Babban sakataren MDD, Antonio Guterres ya yi gargadi a jiya juma’a da safe, akan abinda ya kira ‘yanayi mai  cike da damuwa da yake faruwa a cikin kasar Sudan ta Kudu.

An sami tashin hankali da fadace-fadace a cikin kasar ta Sudan ta kudu a ranar Laraba da jami’an tsaro su ka yi wa mataimakin shugaban kasa na farko Riek Machar daurin talala a cikin gidansa.

Babban magatakardar MDD ya yi kira ga ‘yan siyasar kasar ta Sudan  ta Kudu da su ci gaba da riko da yarjejeniyar sulhu da zaman lafiya,inda ya ce: “ A dawo da gwamnatin hadin kan kasa, da aiki da alkawullan da aka yin a zaman lafiya da sulhu, da hakan ne kadai hanyar dawo da zaman lafiya da kuma yin zabe a cikin watan Disamba 2026.”

A halin da ake ciki a yanzu, kungiyar tarayyar Afirka tana aikin hadin gwiwa da MDD domin kawo karshen  dambaruwar siyasar da ake ciki a kasar.”

Gutrres ya ce; Muna goyon bayan tarayyar Afirka na aikewa da tawagar dattijan nahiyar zuwa Afirka ta kudu da kuma wata tawagar a karkashin jagorancin shugaban kasar Kenya Ruto.

Babban sakataren MDD ya kira yi shugabannin kasar ta Sudan Ta Kudu das u ajiye makamansu na yaki, su kuma bai wa al’ummar kasar fifiko.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut

Jiragen yakin HKI sun kai hari a yankin Hangara dake unguwar “Dhahiya” a cikin birnin Beirut. Yankin da jiragen yakin na ‘yan sahayoniya su ka kai wa harin, yana cike da mutane da kuma makarantu biyu.

Jiragen yakin na HKI sun harba makamai masu linzami 3, da hakan ya haddasa tashin gobara.

A sanadiyyar wannan harin, an sami shahidi daya,yayin da wasu da dama su ka jikkata.

A ranar 1 ga watan Aprilu ma dai sojojin HKI sun kai wani harin a unguwar Dhahiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wasu da dama.

Tun bayan tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Aprilu 2025, HKI ta keta wutar yakin fiye da 2000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut