HausaTv:
2025-07-30@23:35:17 GMT

Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne

Published: 29th, March 2025 GMT

Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro ya bayyana sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da yake ziyarar aiki a kasar Guyana da cewa, sakarai ne.

A yayin ziyarar da sakataren na  harkokin wajen Amurka ya kai zuwa kasar Guyana mai makwabtaka da Venezuela, ya ce, Amurka za ta mayar da martani mai karfi akan Venezuela idan har ta kai wa Guyanan hari.

Rubio ya kara da cewa; Idan haka ta faru, to kuwa Venezuela za ta gwammace kida da karatu a wannan rana.

Amurkan dai ta kulla yarjejeniyar tsaro da kasar ta Guyana a yayin ziyarar da Rubio ya kai.

Shi kuwa shugaban kasar ta Venezuela da yake mayar da martani ya ce; Marco Rubio wawa, ya zo yana yi wa kasar Venezuela barazana daga kasar Guyana, sannan ya kara da cewa; Venezuela ta fi karfin a yi mata barazana, domin ita kasa ce ta ‘yanci.”

Alaka a tsakanin Venezuela ta Amurka ta sake tabarbarewa tun bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulki, bayan da ya kara kakaba mata takunkumai, da kuma batun mayar da ‘yan hijirar kasar daga Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Yemen Zasu Kara Daukan Matakai Kan Jiragen Ruwan Da Ke Hulda Da Isra’ila

Dakarun kasar Yemen sun sanar da sabbin zabukan kara rurutan bude wuta kan makiya a matsayin martani ga abubuwan da suka faru a Gaza

Dakarun sojin kasar Yemen sun bayyana a cikin wata sanarwa da suka fitar a yammacin jiya Lahadi cewa: Suna tunanin zafafa yakin da suke yi da ‘yan mamaya dangane da abin da ke faruwa a Zirin Gaza na kisan kare dangi da kakaba masifar yunwa kan al’ummar yankin.

Rundunar sojin kasar ta Yemen ta tabbatar da fara aikin killace teku kashi na hudu a kan makiya, inda zasu kai hari kan dukkanin jiragen ruwan kamfanonin da ke aiki a tashar jiragen ruwa na Isra’ila, ba tare da la’akari da kasarsu ba, da kuma duk inda sojojin suka isa.

Sanarwar da Rundunar Sojin ta fitar ta ce, bisa la’akari da ci gaban da ake samu a Falastinu da aka mamaye, musamman a zirin Gaza, ci gaba da yakin kisan kiyashi, da kuma shahadar dubun dubatar al’ummar Falastinu sakamakon wuce gona da iri da aka shafe tsawon watanni ana yi, da ke lashe rayukan al’ummar Falasdinu cikin abin kunya na Larabawa, Musulmi da kuma duniya kan irin wannan mummunan shiru, lallai kasar Yemen, zata kalubalanci irin wadannan munanan hare-hare da ake kai wa na kisan kiyashi, wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihin wannan zamani, kasar Yemen ta samu kanta a matsayin wajibin fuskantar wani nauyi na addini da ɗabi’a, da kuma jin kai ga waɗanda ake zalunta a kullum rana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  •  Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
  • Dakarun Yemen Zasu Kara Daukan Matakai Kan Jiragen Ruwan Da Ke Hulda Da Isra’ila