HausaTv:
2025-11-03@02:59:56 GMT

Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025

Published: 29th, March 2025 GMT

A wannan Juma’a ce 28 ga watan Maris na shekarar 2025, aka gudanar da taruka da jerin wano na ranar Qudus ta duniya wadda ta zo daidai da ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan mai alfarma.

An gudanar da wadannan taruka da jerin gwano ne a kasashe daban-daban da suka hada da wasu kasashen musulmi da na larabawa, har da wasu da wasu daga cikin kasashn ymmacin duniya da kuma na Afirka, ta hanyar shirya gagarumin gangamin da ke jaddada aniyarsu ta tabbatar da al’ummar Palastinu ta samu hakkokinta da Haramtacciyar kasar Isra’ila ta haramta musu, tare da nuna cikakken goyon baya ga gwagwarmayarsu ta neman samun wadannan hakkoki nasu.

A safiyar Juma’ar ne aka fara gudanar da jerin gwano na ranar Qudus ta duniya a duk fadin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inda aka samu halartar jama’a da dama karkashin taken “Muna ci gaba da cika alkawarin da muka dauka.” Mahalarta tarukan sun yi tattaki ne daga masallatai da manyan filaye a birane da kauyukan kasar zuwa wuraren da ake gudanar da Sallar Juma’a.

A birnin Mashhad da ke gabashin Iran, tun da sanyin safiya ne aka fara gudanar da jerin gwano a wani bangare na tarukan ranar Kudus da aka saba gudanarwa shekara-shekara.

A birnin Tehran fadar mulkin kasar ta Iran haka lamarin ya kasance, inda tun da jijjfin safiya dubun dubatar jama’a suka fara fita domin isa wurare da aka kebance domin taruwa, kamar yadda aka saba a kowace ana taruwa ne babban titin Inqilab, wanda titi ne da ya kai tsawon fiye da kilo mita goma a tsakiyar birnin Tehran, inda jama’a suka cika wannan titi makil a lokacin gudanar da jerin gwanon ranar Quds ta dunya.

A jajibirin ranar ta Quds Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran Sayyed Ali Khamenei ya bayyana cewa, tattakin ranar Kudus ta duniya na wannan shekara da yardar Allah zai kasance mafi girma a kan na sauran shekaru da suka gabata.

A cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin a daren Alhamis, jagoran ya bayyana cewa, wannan rana a ko da yaushe wata alama ce ta hadin kai da karfin al’umma, yana mai bayyana yadda tattakin ke nuni da cewa al’umma na tare da gwagwarmaya a kan muhimman manufofinta na siyasa, da kuma tsayawa tsayin daka wajen kare hakkokin al’ummar Falastinu.

A kasar Iran dukkanin bangarori na al’umma suna halartar gangamin ranar Quds ta duniya, da hakan ya hada da mabiya addinai daban-daban, da sauran bangarori na al’umma da jami’an gwamnati da ‘yan kasuwa da ma’aikata da ‘yan siyasa da kuma malamai, inda suke haduwa a kan kalma guda guda da manufa guda daya, ita ce nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu, da kuma yin tir da Allawadai da zaluncin Isra’ila a kans, da kuma yin kira da babbar murya a kan wajabcin kare hakkokin wannan al’umma da ake zalunta tsawon shekaru aru-aru.

A sauran bangarori na duniya kuwa, an gudanar da irin wannan gangami da jerin gwano a kasashe daban-daban, yankin Jammu da Kashmir na kasar Indiya, an samu halartar dimbin jama’a da ke daga tutocin Falasdinawa da kuma hotunan masallacin al-aqsa, yayin da suke rera taken ‘Yanci ga Falasdinu.

A kasar Bahrain musamman a yankin Bilad al-Qadeem, mahalarta taron sun daga hotunan Sheikh Isa Qassim, Sheikh Ali Salman, da shahidi Sayyed Hassan Nasrallah, a matsayi alama ta gwagwarmaya da zaluncin Isra’ila da kuma nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu.

A kasar Yemen, kwamitin al-Aqsa, ya kebance dandalin Sabeen da ke babban birnin kasar Sanaa, tare da wurare sama da 400 a fadin larduna 14, a matsayin wuraren da aka gudanar da gagarumin gangami na ranar  Qudus.

Musulmi da kuma masu fafutukar ‘yanci da kare hakkokin bil adama a duniya suna gudanar da ranar Qudus ta duniya kowace shekara a ranar Juma’ar karshe ta Ramadan, inda suke shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga al’ummar Palastinu.

A wasu ƙasashe, ƙungiyoyin zamantakewa daban-daban-ciki har da masana da masu fasaha, suna aiki kafada da kafada don wayar da kan jama’a game da buƙatar tabbatarwa da kiyaye haƙƙin Falasɗinawa ta hanyar gudanar da taruka na kara wa juna sani da laccoci, baje kolin zane-zane, da tattara gudummawa da kayan agaji.

Baya ga sassa na kasashen gabas ta tsakiya da Asia, an gudanar da irin wannan taruka da gangami a wasu kasashen yammacin turai da Amurka da kuma Latin Amurka, da kuma wasu daga cikin kasashen nahiyar Afirka, da suka hada da Najeriya, Tanzania, Ghana, Senegal, Mali, Kenya, Afrka ta kudu da sauransu.

Ana gudanar da ranar Qudus ta duniya ne a ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan bisa kiran da Imam Khumaini ya yi, wanda shi ne ya jagoranci juyin juya halin Musulunci, sannan kuma yunkuri nasa na ayyana ranar Qudus ta duniya, yana a matsayin wani mataki na kare hakkokin al’ummar Palastinu da ‘yancinsu, bayan shafe tsawon shekaru suna cikin wahala da kangi da hijira da mamaye yankunansu, da kuma tuna da duniya irin wannan mawuyacin halin da Isra’ila tare da taimakon kasashen yammacin duniya suka jefa Falastinawa a ciki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ranar Qudus ta duniya da jerin gwano goyon baya ga kare hakkokin

এছাড়াও পড়ুন:

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

Imam Ali shi ne halifan Annabi Muhammad na hudu a mahangar Ahlussunnan, amma mabiya mazhabar Shi’a na daukar sa a matsayin na farko daga cikin imamansu 12.

Wannan ya sanya akasarin mabiya Shi’a na Iraki kan bukaci a binne su a makabartar, kuma sanadiyyar saukin sufuri a zamunnan baya-bayan nan, wasu mabiya Shi’a daga kasashen duniya kan so a binne su a makabartar.

Tsarin makabartar ya kasance cakuduwa ce ta gine-ginen hubbarai irin na zamanin baya, da hanyoyi masu tsuku da suka ratsa ta cikinta da kuma wasu wurare da ake yi wa kallon masu tsarki.

 

Me ya sa ake kiran makabartar Wadi al-Salam?

Ana kiran makabartar da sunan Wadi al-Salam, wato ‘kwarin aminci’ ne saboda dalilai na tarihi da dama.

Dalilai na addini: Ana yi wa makabartar daukar mai daraja, tare da imanin cewa wadanda ke kwance a cikinta na cikin rahama.

Alaka da Imam Ali: Makabartar tana makwaftaka da kabarin Imam Ali bin Abi Talib a birnin Najaf, wanda hakan ya sa Musulmai, musamman mabiya akidar Shi’a ke girmama ta kuma suke kwadayin ganin an binne su a cikinta.

Girma: Makabartar ta kasance mafi girma a duniya, inda ta mamaye wuri mai girman gaske, kunshe da miliyoyin kaburbura, inda ta zamo tamakar wani birni na mamata.

Ziyara: Masu ziyara zuwa birnin Najaf, mai tsarki ga mabiya akidar Shi’a sukan bi ta cikin makabartar tare da karanta Fatiha da kuma yin addu’o’in samun rahama ga wadanda ke kwance, lamarin da ya mayar da wurin tamkar wuri na ziyarar ibada.

Wadannan dalilai ne suka sanya tuntuni aka yi wa wurin lakabi da ‘kwarin aminci’ tun asali, kuma ake ci gaba da kiranta da hakan har yanzu.

 

Tarihin kafuwar makabartar Wadi al-Salam

Makabartar ta samo asali ne tun kafin zuwan addinin Musulunci a lokacin Annabi Muhammad, inda tun kafin wancan lokaci ake binne mutane a wurin.

Wuri ne mai muhimmanci wanda ke karbar bakuncin masu bincike na kimiyya da masana addini, musamman mabiya Shi’a daga sassa daban-daban na duniya.

Wadi al-Salam na da kofofi da dama da ake bi wajen shigar ta, inda hakan ke saukake zirga-zirga ga masu ziyara, kuma yawancin wadannan kofofi na karuwa ne bisa fadadar makabartar.

A shekara ta 2016 ne Hukumar kula da ilimi da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana makabartar a matsayin daya daga cikin wuraren tarihi na duniya.

 

Kalubalen da makabartar ke fuskanta

Daya daga cikin manyan kalubalen da makabartar ke fuskanta shi ne karuwar mutane da ake binnewa a lokacin yaki.

Misali, a lokacin da aka yi fama da rikicin kungiyar ISIS a Iraki, yawan mutanen da ake binnewa a kowace rana a makabartar ya daga zuwa 150 ko 200 a kowace rana, daga gawa 80 zuwa 120 da aka saba.

Wannan ya sanya wuraren binne sabbin mamata ya yi karanci.

 

Farashin binne mamaci

Farashin binne mamaci a makabartar Wadi al-Salam ya danganta ne da lokaci da kuma halin da ake ciki na zaman lafiya.

Ya zuwa farkon shekara ta 2025, kudin sayen filin binne mamaci mai girman murabba’in mita 25 ya kai miliyan biyar na kudn kasar Iraki, wato kimanin Dala 4,100, inda hakan ya nunka farashin da ake biya a lokutan da ake zaman lumana sosai.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda