HausaTv:
2025-07-31@08:53:26 GMT

Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025

Published: 29th, March 2025 GMT

A wannan Juma’a ce 28 ga watan Maris na shekarar 2025, aka gudanar da taruka da jerin wano na ranar Qudus ta duniya wadda ta zo daidai da ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan mai alfarma.

An gudanar da wadannan taruka da jerin gwano ne a kasashe daban-daban da suka hada da wasu kasashen musulmi da na larabawa, har da wasu da wasu daga cikin kasashn ymmacin duniya da kuma na Afirka, ta hanyar shirya gagarumin gangamin da ke jaddada aniyarsu ta tabbatar da al’ummar Palastinu ta samu hakkokinta da Haramtacciyar kasar Isra’ila ta haramta musu, tare da nuna cikakken goyon baya ga gwagwarmayarsu ta neman samun wadannan hakkoki nasu.

A safiyar Juma’ar ne aka fara gudanar da jerin gwano na ranar Qudus ta duniya a duk fadin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inda aka samu halartar jama’a da dama karkashin taken “Muna ci gaba da cika alkawarin da muka dauka.” Mahalarta tarukan sun yi tattaki ne daga masallatai da manyan filaye a birane da kauyukan kasar zuwa wuraren da ake gudanar da Sallar Juma’a.

A birnin Mashhad da ke gabashin Iran, tun da sanyin safiya ne aka fara gudanar da jerin gwano a wani bangare na tarukan ranar Kudus da aka saba gudanarwa shekara-shekara.

A birnin Tehran fadar mulkin kasar ta Iran haka lamarin ya kasance, inda tun da jijjfin safiya dubun dubatar jama’a suka fara fita domin isa wurare da aka kebance domin taruwa, kamar yadda aka saba a kowace ana taruwa ne babban titin Inqilab, wanda titi ne da ya kai tsawon fiye da kilo mita goma a tsakiyar birnin Tehran, inda jama’a suka cika wannan titi makil a lokacin gudanar da jerin gwanon ranar Quds ta dunya.

A jajibirin ranar ta Quds Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran Sayyed Ali Khamenei ya bayyana cewa, tattakin ranar Kudus ta duniya na wannan shekara da yardar Allah zai kasance mafi girma a kan na sauran shekaru da suka gabata.

A cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin a daren Alhamis, jagoran ya bayyana cewa, wannan rana a ko da yaushe wata alama ce ta hadin kai da karfin al’umma, yana mai bayyana yadda tattakin ke nuni da cewa al’umma na tare da gwagwarmaya a kan muhimman manufofinta na siyasa, da kuma tsayawa tsayin daka wajen kare hakkokin al’ummar Falastinu.

A kasar Iran dukkanin bangarori na al’umma suna halartar gangamin ranar Quds ta duniya, da hakan ya hada da mabiya addinai daban-daban, da sauran bangarori na al’umma da jami’an gwamnati da ‘yan kasuwa da ma’aikata da ‘yan siyasa da kuma malamai, inda suke haduwa a kan kalma guda guda da manufa guda daya, ita ce nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu, da kuma yin tir da Allawadai da zaluncin Isra’ila a kans, da kuma yin kira da babbar murya a kan wajabcin kare hakkokin wannan al’umma da ake zalunta tsawon shekaru aru-aru.

A sauran bangarori na duniya kuwa, an gudanar da irin wannan gangami da jerin gwano a kasashe daban-daban, yankin Jammu da Kashmir na kasar Indiya, an samu halartar dimbin jama’a da ke daga tutocin Falasdinawa da kuma hotunan masallacin al-aqsa, yayin da suke rera taken ‘Yanci ga Falasdinu.

A kasar Bahrain musamman a yankin Bilad al-Qadeem, mahalarta taron sun daga hotunan Sheikh Isa Qassim, Sheikh Ali Salman, da shahidi Sayyed Hassan Nasrallah, a matsayi alama ta gwagwarmaya da zaluncin Isra’ila da kuma nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu.

A kasar Yemen, kwamitin al-Aqsa, ya kebance dandalin Sabeen da ke babban birnin kasar Sanaa, tare da wurare sama da 400 a fadin larduna 14, a matsayin wuraren da aka gudanar da gagarumin gangami na ranar  Qudus.

Musulmi da kuma masu fafutukar ‘yanci da kare hakkokin bil adama a duniya suna gudanar da ranar Qudus ta duniya kowace shekara a ranar Juma’ar karshe ta Ramadan, inda suke shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga al’ummar Palastinu.

A wasu ƙasashe, ƙungiyoyin zamantakewa daban-daban-ciki har da masana da masu fasaha, suna aiki kafada da kafada don wayar da kan jama’a game da buƙatar tabbatarwa da kiyaye haƙƙin Falasɗinawa ta hanyar gudanar da taruka na kara wa juna sani da laccoci, baje kolin zane-zane, da tattara gudummawa da kayan agaji.

Baya ga sassa na kasashen gabas ta tsakiya da Asia, an gudanar da irin wannan taruka da gangami a wasu kasashen yammacin turai da Amurka da kuma Latin Amurka, da kuma wasu daga cikin kasashen nahiyar Afirka, da suka hada da Najeriya, Tanzania, Ghana, Senegal, Mali, Kenya, Afrka ta kudu da sauransu.

Ana gudanar da ranar Qudus ta duniya ne a ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan bisa kiran da Imam Khumaini ya yi, wanda shi ne ya jagoranci juyin juya halin Musulunci, sannan kuma yunkuri nasa na ayyana ranar Qudus ta duniya, yana a matsayin wani mataki na kare hakkokin al’ummar Palastinu da ‘yancinsu, bayan shafe tsawon shekaru suna cikin wahala da kangi da hijira da mamaye yankunansu, da kuma tuna da duniya irin wannan mawuyacin halin da Isra’ila tare da taimakon kasashen yammacin duniya suka jefa Falastinawa a ciki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ranar Qudus ta duniya da jerin gwano goyon baya ga kare hakkokin

এছাড়াও পড়ুন:

Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku

Ministocin harkokin wajen kasar Siriya da kuma na HKI zasu gudanar da taro a birnin Baku na kasar Azarbaijan a ranar Alhamis mai zuwa don tattauna maganar tsaro a kasar Siriya kamar yadda suka fada.

Shafin yanar gizo na labarai ArabNews na kasar Saudiya ya bayyana cewa Asaad Al-Shaibani ministan harkokin wajen kasar Siriya da kuma ministan ayyuka na musamman na HKI Ron Dermer sun gudanar da taro a birnin Paris na kasar faransa a cikinn yan kwanakin da suka gabata, a halin yanzu kuma zasu gudanar da taron a birnin Baku na kasar Azrbaijan a ranar Alhamis mai zuwa.

Labarin ya kara da cewa kafin haka dai Al-Shaibani ya ziyarci Moscow kamar yadda wata majiya wacce bata son a bayyana sunanta fadawa Arabnews.

Kafin haka dai muna iya cewa HKI tana yaki da kasar Siriya tun shekara 1948 wato a lokacinda turawan Ingila suka kafata., har zuwa watan decemban shekara ta 2024 a lokacinda kasashen yankin suka taimakawa kungiyar yan ta’adda ta HTS ta han kan kujerar shugaban kasar.

Sai dai masana da dama suna ganin da wuya a ce taron kasashen biyu bai shafi kasar Iran ba. Don idan batun kasar Siriya ce me ya hada siriya da Baku.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500