Aminiya:
2025-07-31@18:24:59 GMT

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno

Published: 29th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Jama’atul Nasrul Islam (JNI) , ta raba kayayyaki da sauran kyatuttukan Sallah ga marayu 50 gabanin bikin Sallah ƙarama a garin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

An gudanar da bikin ba da tallafin ne a harabar makarantar sakandare ta Bulabulin da ke birnin na Maiduguri.

Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna

Da yake jawabi a wajen taron, mataimakin daraktan kungiyar JNI reshen Maiduguri, Malam Ibrahim M.

Bello, ya jaddada muhimmancin tallafa wa mabuƙata, yana mai jaddada cewa wannan shi ne babban burin ƙungiyar.

Ya buƙaci waɗanda suka samu tallafin da su yi amfani da kyaututtukan domin biyan buƙatunsu.

A nasa jawabin, mataimakin sakataren ƙungiyar, Abubakar Abdullahi, ya ce sun yi hakan ne da nufin sanya farin ciki da jin dadi ga yara marasa galihu a lokacin bukukuwan Sallah.

Ƙungiyar ta JNI ta himmatu matuƙa wajen taimaka wa mabuƙata, musamman marayu da ba su da abin dogaro da kai in ji Abubakar.

Ya kara bayyana cewa, an zabo waɗanda suka samu tallafin ne bisa sharuɗan da hukumar gudanarwar ƙungiyar ta gindaya.

A cewarsa, ƙungiyar ta shafe sama da shekaru goma tana gudanar da irin waɗannan ayyuka na agaji.

Abdullahi ya kuma yi kira ga iyaye, hukumomin gwamnati, da shugabannin masana’antu da su haɗa hannu wajen ganin an samu sauƙaƙa rayuwar marayu.

Ya yi nuni da cewa, wannan ƙoƙari na haɗin gwiwa zai taimaka matuƙa wajen tallafa wa yara masu rauni da kuma inganta fahimtar al’umma dangane da zamantakewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno kayan Sallah Marayu

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Gwamnan Jihar Filato, Barr. Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa babu wata ƙaramar hukuma a cikin jihar da ƴan ta’adda ko ƴan bindiga ke da iko da ita. Ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ƴan jarida da aka gudanar a sabon gidan gwamnati da ke Little Rayfield, Jos, a ranar Talata.

Gwamna Mutfwang ya ce gwamnatinsa ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar tsaro, musamman ta hanyar farfaɗo da rundunar tsaron cikin gida ta jihar wato Operation Rainbow, domin tallafa wa sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen ganin an dawo da zaman lafiya a sassan jihar da rikice-rikicen ƙabilanci ko na addini suka taɓa. Ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya domin tabbatar da fahimtar juna da daidaiton al’umma.

Gwamnan ya sake jaddada buƙatar kafa ƴansandan jiha, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a faɗin Nijeriya. Ya ce kafa ƴansandan jiha zai bai wa gwamnatocin jihohi damar yin tsari da ɗaukar matakan da suka dace da yanayin tsaron yankunansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza