Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno
Published: 29th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Jama’atul Nasrul Islam (JNI) , ta raba kayayyaki da sauran kyatuttukan Sallah ga marayu 50 gabanin bikin Sallah ƙarama a garin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.
An gudanar da bikin ba da tallafin ne a harabar makarantar sakandare ta Bulabulin da ke birnin na Maiduguri.
Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da OsasunaDa yake jawabi a wajen taron, mataimakin daraktan kungiyar JNI reshen Maiduguri, Malam Ibrahim M.
Ya buƙaci waɗanda suka samu tallafin da su yi amfani da kyaututtukan domin biyan buƙatunsu.
A nasa jawabin, mataimakin sakataren ƙungiyar, Abubakar Abdullahi, ya ce sun yi hakan ne da nufin sanya farin ciki da jin dadi ga yara marasa galihu a lokacin bukukuwan Sallah.
Ƙungiyar ta JNI ta himmatu matuƙa wajen taimaka wa mabuƙata, musamman marayu da ba su da abin dogaro da kai in ji Abubakar.
Ya kara bayyana cewa, an zabo waɗanda suka samu tallafin ne bisa sharuɗan da hukumar gudanarwar ƙungiyar ta gindaya.
A cewarsa, ƙungiyar ta shafe sama da shekaru goma tana gudanar da irin waɗannan ayyuka na agaji.
Abdullahi ya kuma yi kira ga iyaye, hukumomin gwamnati, da shugabannin masana’antu da su haɗa hannu wajen ganin an samu sauƙaƙa rayuwar marayu.
Ya yi nuni da cewa, wannan ƙoƙari na haɗin gwiwa zai taimaka matuƙa wajen tallafa wa yara masu rauni da kuma inganta fahimtar al’umma dangane da zamantakewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Borno kayan Sallah Marayu
এছাড়াও পড়ুন:
Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
Ministan harkokin wajen Omani Badr Albusaidi ya sanar da cewa, ba za a gudanar da zagaye na shida na tattaunawar nukiliya tsakanin Iran da Amurka ba.
Yau Lahadi ne aka shirya gudanar da zagaye na gaba na shawarwari a Muscat babban birnin kasar Oman.
A cikin wani sakon da ya wallafa a kan X (tsohon Twitter), Albusaidi ya tabbatar da sokewar, yayin da ya jaddada cewa “diflomasiyya da tattaunawa sun kasance hanya daya tilo ta samun zaman lafiya mai dorewa.”
“Tattaunawar Iran da Amurka, wadda aka shirya gudanar da ita a birnin Muscat ranar Lahadin nan, ba za ta gudana a yanzu ba.
Tattaunawar diflomasiyyar da aka faro kan shirin nukiliyar Iran, a watan Afrilu a shiga tsakanin masarautar Oman, ta wargaje biyo bayan mummunan harin da Isra’ila ta kai kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugabar harkokin wajen kungiyar EU Kaja Kalas a ranar Asabar, ya ce ci gaba da tattaunawa da Amurka a cikin danyen aikin da Isra’ila ke yi bai da wata fa’ida.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce kalaman shugaban Amurka sun tabbatar da cewa matakin da Isra’ila ta dauka kan Iran ya samo asali ne daga goyon bayan da Washington ke baiwa gwamnatin Tel-Aviv kai tsaye.