Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-16@23:06:11 GMT

Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria

Published: 2nd, March 2025 GMT

Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria

Malamai daga makarantun firamare 116 dake karamar hukumar Zaria sun gudanar da taron addu’o’i na musamman ga shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen da gwamnatin jihar Kaduna.

Malaman sun gudanar da addu’o’in ne domin nuna farinciki da godiya bisa yadda suke matukar kula da ilimi,wanda hakan ya inganta harkokin ilimin kuma ya kara bunkasa jin dadin Malaman yankin.

Sakatariyar ilimi ta karamar hukumar Zaria, Dr Hassana Lawal ta shedawa manema labaru lokacin addu’o’in a zaria cewa a kalla Malaman makarantun firamare 2,225 ne suka amfana da tallafin kayan abinci domin gudanar da azumin watan Ramadan.

A cewar ta,kayan abincin sun hada da kilo 25 na shinkafa da lita 4 na man gyada da fakitin tafiya da kuma kilo 10 na buhun garin samabita.

“Wannan shine karo na 8 da shugaban majalisar wakilan ya baiwa malaman makarantar firamaren irin wannan tallafin tun daga lokacin da hau karagar shugabancin majalisar.

“Baya ga tallafin kayan abinci,ya baiwa duk shugabannin makarantun firamare 116 da ke yankin kyautar babura domin saukaka masu zuwa wurin aiki,wanda a cewar ta abin godiya ne matuka”.

Haka kuma sakatariyar ilimin ta yaba da kokarin da gwamnan jihar kaduna, Malam Uba Sani ke yi na bunkasa ilimi a jihar.

Dr Lawal ta ce kokarin da gwamnan ke yi sun kushi gina ajujuwa 12 a makarantun firamare da dama a karamar hukumar Zaria baya ga tallafin kayan karatu, wanda hakan ne yasa dole su yi masu addu’o’in.

Ta kara da cewa Malaman sun zami watan Ramadan ne domin gudanar da addu’o’in Allah ya baiwa shugaban majalisar wakilai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi nasara da kwarin gwiwa wajen ci gaba da bunkasa ilimi a jihar.

A nashi jawabin, sakataren Kungiyar malamai na karamar hukumar Zaria, Malam Kasimu Mohammed ya ce tallafin kayan abincin ya taimaka wa Malaman matukar gaske.

A don haka sai ya bukaci sauran yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi shugaban majalisar wakilan ta hanyar tallafawa Malaman makarantun firamare a yankunan su.

Haliru Hamza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Furame Zaria karamar hukumar Zaria makarantun firamare shugaban majalisar tallafin kayan

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Yahudawan sahayoniyya sun kashe adadi mai yawa na yaran Iran a cikin ta’addancin da suke yi 

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe kananan yara masu yawa na Iran a cikin wannan ta’asa da take gudanarwa kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A cikin wani sako da Ismail Baqa’i ya rubuta a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana cewa: “Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe adadi mai yawa na yara Iraniyawa tare da kai hari kan asibitin yara a tsawon kwanaki uku na hare-haren soji kan Iran. Kamar yadda Ya’ir Golan, tsohon mataimakin hafsan hafsoshin sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila ya amince da cewa: Kashe yara wani nau’i ne na nishaɗi a gare su.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai