Aminiya:
2025-09-18@00:54:36 GMT

Ban fitar da ran lashe Premier League na bana ba — Arteta

Published: 2nd, March 2025 GMT

Mikel Arteta ya ce, Arsenal ce za ta lashe kofin Premier League na kakar bana, ba kamar yadda ake hasashen Liverpool ba.

A ranar Laraba Gunners, wadda take da tazarar maki 11 tsakaninta da Liverpool za ta fafata da Nottingham Forest a wasan mako na 27 a Premier League.

Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta? An kama ɓarayin waya a Kano

A ranar Lahadin makon da ya gabata, Liverpool ta yi nasara a kan Manchester City da 2-0 a Etihad, bayan Arsenal ta yi rashin nasara 1-0 ranar Asabar a Emirates ta hannun West Ham.

Bayan wasan na West Ham Mikel Arteta ya zargi ‘yan wasan da rashin sa ƙwazo a fafatawar, bayan Gunners shafe kaka 21 rabon ta da kofin Premier League.

Kociyan ɗan kasar Sifaniya ya kara da cewa, ‘‘Damar ɗaukar babban kofin tamaula na Ingila na bana ba a hannuna yake ba.’’

To sai dai a shirin da Arsenal ke yi na karawa da Forest a ranar Laraba, Arteta ya ce, ba zai taɓa fitar da ran lashe kofin Premier na kakar bana ba.

Arsenal wadda take sa ran ɗaukar Premier na kakar bana ta gamu da koma-baya, saboda wasu ’yan wasanta da ke jinya.

Kai Havertz da Gabriel Jesus za su ci gaba da jinya har bayan kakar bana, ana sa ran Bukayo Saka zai koma taka leda a cikin watan Maris.

Rabon da Saka ya buga wa Arsenal tamaula tun cikin Disamba, shi kuwa Gabriel Martinelli na ci gaba da jinya.

Kyaftin Odegaard ya yi jinyar da bai buga wasa 12 ba tun farkon fara wasannin bana, inda kuma aka dakatar da wasu ’yan wasan Gunners.

’Yan wasa biyar na Arsenal aka bai wa jan kati a wasa 26 a Premier League kawo yanzu.

Arsernal ta daɗe tana biye da Liverpool a teburin Premier League, wanda tuni Gunners ta kai zagaye na biyu a Champions League, amma an yi waje da ita a FA da Carabao Cup.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arsenal Mikel Arteta

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Barcelona ta koma matsayi na biyu a kan teburin gasar La Liga ta Sifaniya bayan ta lallasa ƙungiyar Valencia a filin wasa na Johan Cruyff da ke birnin Barcelona.

Fermin Lopez, Raphinha da Lewandowski ne suka zura ƙwallaye shida a ragar Valencia a wasan da aka buga da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya. Da wannan nasara, Ƙungiyar da Hansi Flick ke jagoranta ta tara maki 10 a cikin wasanni huɗu da ta buga a gasar.

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

An yi tsammanin Barcelona za ta fara buga wasan gidanta a sabon filin Spotify Camp Nou da aka gyara, amma sai mahukuntan Ƙungiyar suka yanke shawarar yin wasan a filin Johan Cruyff mai ƙarfin ɗaukar ‘yan kallo 6,000 kacal, wanda mafi yawan lokuta Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta mata Barcelona ke amfani da shi.

A gaba kuma, Barcelona za ta bakunci Newcastle United a filin wasa na St James’ Park a zagayen farko na gasar Zakarun Turai (UEFA Champions League) a ranar 18 ga Satumba. A gefe guda, Valencia za ta karɓi baƙuncin Atletico Bilbao a wasan mako na biyar na La Liga a ranar 20 ga Satumba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff