KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
Published: 16th, June 2025 GMT
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kaduna (KADSEMA), tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM), sun fara aikin tantance ɓarnar da ambaliya da iska suka yi a yankunan Kudancin Kaduna.
Manufar aikin ita ce su tattara sahihan bayanai daga jama’a da shugabanninsu domin a samu taimako da kuma tsara hanyoyin kare aukuwar hakan a gaba.
Yayin da suka kai ziyara Ƙaramar Hukumar Jama’a, Ko’odinetan KADSEMA na Kudancin Kaduna, Mista Ayyuka Shemang, ya ce sun fara wannan aiki ne saboda hasashen ambaliya daga Hukumar Yanayi ta Najeriya (NiMet).
Ya jaddada muhimmancin shirye-shirye tun kafin saukar daminar bana.
Shugaban tawagar IOM a Kaduna, Arhyel Mbaya, ya ce wannan aiki yana da muhimmanci don a tabbatar da cewa waɗanda ambaliya da iska suka shafa sun samu taimako yadda ya kamata.
Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Jama’a, Emmanuel Moses Utung, ya yaba da aikin, inda ya ce sun riga sun umarci kansiloli su tattara bayanai daga mazaɓunsu.
Tawagar ta haɗa da wakilai daga Red Cross, kafafen watsa labarai, ƙungiyoyin addini, sarakunan gargajiya da jami’an gwamnati.
Waɗannan na taimakawa wajen tabbatar da cewa an gano duk wuraren da abin ya shafa.
Ana sa ran bayanan da za a samu daga wannan aiki za su taimaka wajen tsara agajin gaggawa da kuma shirye-shiryen don tunkarar sauyin yanayi a Kudancin Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Barna
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kano, Alhaji Salim Hashim Idris Gwangwazo, ya kaddamar da shirin kula da ido kyauta domin tallafawa jama’a da ke fama da ‘Glaucoma’ da ke lalata rijiyoyin ido, da ‘Cataract’ wato yanar ido da sauran cututtukan ido.
An gudanar da shirin ne a Asibitin Kwalli tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Hukumar Lafiyar Farko ta Jiha, da ƙaramar hukumar da masu bada tallafi daga kasashen waje.
Shirin ya haɗa da gwaje-gwajen lafiyar ido, da bayar da magunguna da kuma rarraba tabarau kyauta, musamman ga marasa ƙarfi a cikin al’umma.
Shugaban ƙaramar hukumar, ta bakin Kwamishinan Lafiya Alhaji Mustapha Darma, ya bukaci jama’a da su ci gaba da tallafawa gwamnati wajen samar da ingantaccen kulawa.
A baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta dauki nauyin kula da lafiyar ido ga mutum sama da 500 daga Birnin Kano da sauran kananan hukumomi.
Shugaban kula da lafiya am matakin farko na ƙaramar hukumar, Alhaji Lawan Jafar, ya ce wadanda lalurar su ba ta tsananta ba za a ba su shawarwarin kula da lafiyar su, da magunguna, wa su ma har da tabarau, yayin da wadanda ta su ta tsananta kuma za a musu tiyata.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun nuna godiya tare da yi wa gwamnati addu’a don samun nasara.
Shugaban tawagar likitocin, Dr. Kamal Saleh, ya tabbatar da cewa shirin ya samu nasara sosai.
Daga Khadijah Aliyu