Aminiya:
2025-07-31@22:33:23 GMT

KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna

Published: 16th, June 2025 GMT

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kaduna (KADSEMA), tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM), sun fara aikin tantance ɓarnar da ambaliya da iska suka yi a yankunan Kudancin Kaduna.

Manufar aikin ita ce su tattara sahihan bayanai daga jama’a da shugabanninsu domin a samu taimako da kuma tsara hanyoyin kare aukuwar hakan a gaba.

Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba

Yayin da suka kai ziyara Ƙaramar Hukumar Jama’a, Ko’odinetan KADSEMA na Kudancin Kaduna, Mista Ayyuka Shemang, ya ce sun fara wannan aiki ne saboda hasashen ambaliya daga Hukumar Yanayi ta Najeriya (NiMet).

Ya jaddada muhimmancin shirye-shirye tun kafin saukar daminar bana.

Shugaban tawagar IOM a Kaduna, Arhyel Mbaya, ya ce wannan aiki yana da muhimmanci don a tabbatar da cewa waɗanda ambaliya da iska suka shafa sun samu taimako yadda ya kamata.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Jama’a, Emmanuel Moses Utung, ya yaba da aikin, inda ya ce sun riga sun umarci kansiloli su tattara bayanai daga mazaɓunsu.

Tawagar ta haɗa da wakilai daga Red Cross, kafafen watsa labarai, ƙungiyoyin addini, sarakunan gargajiya da jami’an gwamnati.

Waɗannan na taimakawa wajen tabbatar da cewa an gano duk wuraren da abin ya shafa.

Ana sa ran bayanan da za a samu daga wannan aiki za su taimaka wajen tsara agajin gaggawa da kuma shirye-shiryen don tunkarar sauyin yanayi a Kudancin Kaduna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Barna

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.

A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati