A wani bidiyo mai ban mamaki da Hukumar Kashe Gobara ta yankin Tulsa da ke kasar Amurka ta fitar ya nuna yadda wani kare ya yi sanadin tashin wuta a wani gida ta hanyar tauna fakitin batirin Lithium.
Hukuma ta kama karen bayan gano hakan a bidiyon mai ban mamaki, wanda ya nuna shi yana tauna fakitin batirin lithium-ion wanda mai shi ya bari.
Bayan dan lokaci da fara taunawa, baturin ya fara tarwatsin wuta, sannan ya yi bindiga, lamarin da ya sa karen da wata kyanwa da ke kwana a kusa da gidan tserewa don tsira da rayukansu.
An yi sa’a, duk dabbobin sun tsere ta kofar gidan, wutar ba ta yi musu lahani ba, amma gobarar ta yi mummunar barna a gidan.
Masu kashe gobara a yanzu suna amfani da bidiyon a matsayin gargaɗi game da barin batir lithium a wurin da yara da dabbobi za su iya kaiwa.
Mai magana da yawun Ma’aikatar Kashe Gobara ta Tulsa ya ce, duk da irin barnar da gobarar ta yi, abubuwa na iya zama mafi muni idan akwai mutane da ke kwana a ciki, ko kuma yadda za a iya tsira da dabbobi marasa galihu.
“Lokacin da wannan wutar batirin ta fara ba tare da katsewa ba, ta haifar da zafi da samar da iskar gas mai konewa da guba har ma da tartsatsi,” in ji daya daga cikin ma’aikatar kashe gobaran, Andy Little game da makamashin da yake cikin kananan baturan lithium.
Ya ce, “Yana da mahimmanci ku bi ka’idojin masana’anta lokacin amfani da baturan lithium-ion, kawai amfani da caja da aka yarda da su da adana su a wajen da yara da dabbobin gida.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe.
Rundunar ’yan sanda ta Jihar, ta tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Asabar.
Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan AmurkaA cewar sanarwar, Abba Hassan, wanda asalinsa ɗa Jihar Borno ne, ya gudu daga gidan yarin a ranar 31 ga watan Oktoba, bayan kotu ta yanke masa hukuncin kisa.
DSP Abdulkarim, ya roƙi jami’an tsaro, direbobi, sarakunan gargajiya, ’yan banga da al’ummomin Jihar Yobe da maƙwabtan jihohi da su taimaka da bayanai da za su taimaka wajen sake kama shi.
Ya kuma gargaɗi jama’a da kada su kusanci fursunan da ya tsere, domin hakan na iya zama hatsari.
“Domin kare lafiyarku, idan kuka ga wani da kuke zargi shi ne, ku sanar da ofishin ’yan sanda mafi kusa ko gidan gyaran hali, ko kuma ku kira lambar 08038452982,” in ji sanarwar.