A wani bidiyo mai ban mamaki da Hukumar Kashe Gobara ta yankin Tulsa da ke kasar Amurka ta fitar ya nuna yadda wani kare ya yi sanadin tashin wuta a wani gida ta hanyar tauna fakitin batirin Lithium.
Hukuma ta kama karen bayan gano hakan a bidiyon mai ban mamaki, wanda ya nuna shi yana tauna fakitin batirin lithium-ion wanda mai shi ya bari.
Bayan dan lokaci da fara taunawa, baturin ya fara tarwatsin wuta, sannan ya yi bindiga, lamarin da ya sa karen da wata kyanwa da ke kwana a kusa da gidan tserewa don tsira da rayukansu.
An yi sa’a, duk dabbobin sun tsere ta kofar gidan, wutar ba ta yi musu lahani ba, amma gobarar ta yi mummunar barna a gidan.
Masu kashe gobara a yanzu suna amfani da bidiyon a matsayin gargaɗi game da barin batir lithium a wurin da yara da dabbobi za su iya kaiwa.
Mai magana da yawun Ma’aikatar Kashe Gobara ta Tulsa ya ce, duk da irin barnar da gobarar ta yi, abubuwa na iya zama mafi muni idan akwai mutane da ke kwana a ciki, ko kuma yadda za a iya tsira da dabbobi marasa galihu.
“Lokacin da wannan wutar batirin ta fara ba tare da katsewa ba, ta haifar da zafi da samar da iskar gas mai konewa da guba har ma da tartsatsi,” in ji daya daga cikin ma’aikatar kashe gobaran, Andy Little game da makamashin da yake cikin kananan baturan lithium.
Ya ce, “Yana da mahimmanci ku bi ka’idojin masana’anta lokacin amfani da baturan lithium-ion, kawai amfani da caja da aka yarda da su da adana su a wajen da yara da dabbobin gida.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.