Leadership News Hausa:
2025-11-03@08:56:20 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Published: 2nd, March 2025 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta gamu da cikas a kokarinta na darewa kan teburin gasar Laliga ta kasar Sifaniya, bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Real Betis a filin wasa na Benito Villamarin da ke Seville.

Tsohon dan wasan Real Madrid, Isco Alacon ne ya lashe kyautar gwarzon dan wasa a wasan na ranar Asabar.

Isco ya na daya daga cikin ‘yan wasan da suka lashe kofin Turai biyar tare da Real Madrid.

Barcelona Na Cigaba Da Matsawa Real Madrid Lamba Mbappe Da Bellingham Ba Za Su Buga Wasan Da Real Madrid Za Ta Kara Da Leganes Ba

Real Madrid ce ta fara jefa kwallo ta hannun Brahim Diaz, kafin Johnny Cardoso ya farke wa masu masaukin bakin ana dab-da tafiya hutun rabin lokaci, Isco ya mayar da wasan danye bayan kwallon da ya jefa a minti na 54 da fara wasan.

Real Madrid wadda ke matsayi na biyu a gasar La Liga, sun buga wasanni 26, inda su ka samu nasara a wasanni 16, aka buga canjaras a wasanni 6, yayin da aka doke ta a wasanni 4.

Isco wanda ya shafe shekaru 9 a Santiago, ya jagoranci ‘yan wasan Betis a matsayin kyaftin a wasan na mako na 26.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe

Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe.

Rundunar ’yan sanda ta Jihar, ta tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Asabar.

Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

A cewar sanarwar, Abba Hassan, wanda asalinsa ɗa  Jihar Borno ne, ya gudu daga gidan yarin a ranar 31 ga watan Oktoba, bayan kotu ta yanke masa hukuncin kisa.

DSP Abdulkarim, ya roƙi jami’an tsaro, direbobi, sarakunan gargajiya, ’yan banga da al’ummomin Jihar Yobe da maƙwabtan jihohi da su taimaka da bayanai da za su taimaka wajen sake kama shi.

Ya kuma gargaɗi jama’a da kada su kusanci fursunan da ya tsere, domin hakan na iya zama hatsari.

“Domin kare lafiyarku, idan kuka ga wani da kuke zargi shi ne, ku sanar da ofishin ’yan sanda mafi kusa ko gidan gyaran hali, ko kuma ku kira lambar 08038452982,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA