Leadership News Hausa:
2025-08-01@13:46:46 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Published: 2nd, March 2025 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta gamu da cikas a kokarinta na darewa kan teburin gasar Laliga ta kasar Sifaniya, bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Real Betis a filin wasa na Benito Villamarin da ke Seville.

Tsohon dan wasan Real Madrid, Isco Alacon ne ya lashe kyautar gwarzon dan wasa a wasan na ranar Asabar.

Isco ya na daya daga cikin ‘yan wasan da suka lashe kofin Turai biyar tare da Real Madrid.

Barcelona Na Cigaba Da Matsawa Real Madrid Lamba Mbappe Da Bellingham Ba Za Su Buga Wasan Da Real Madrid Za Ta Kara Da Leganes Ba

Real Madrid ce ta fara jefa kwallo ta hannun Brahim Diaz, kafin Johnny Cardoso ya farke wa masu masaukin bakin ana dab-da tafiya hutun rabin lokaci, Isco ya mayar da wasan danye bayan kwallon da ya jefa a minti na 54 da fara wasan.

Real Madrid wadda ke matsayi na biyu a gasar La Liga, sun buga wasanni 26, inda su ka samu nasara a wasanni 16, aka buga canjaras a wasanni 6, yayin da aka doke ta a wasanni 4.

Isco wanda ya shafe shekaru 9 a Santiago, ya jagoranci ‘yan wasan Betis a matsayin kyaftin a wasan na mako na 26.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

 

Dandali na NINAuth, wanda NIMC ya tsara kuma ya aiwatar, yana bayar da damar tantance bayanan ‘yan kasa ta hanya mafi dacewa da aminci don tabbatar da asalinsu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC
  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
  • Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso