Leadership News Hausa:
2025-10-31@09:11:19 GMT

Zanga-zangar Lumana Wani Bangare Ne Na Mulkin Dimokuradiyya

Published: 25th, April 2025 GMT

Zanga-zangar Lumana Wani Bangare Ne Na Mulkin Dimokuradiyya

Irin wannan zanga-zangar, ta sha ban-ban, da irin wadda ake gudanawar a kasashen da suka ci gaba kuma suke gudanar da mulki, irin na Dimokiradiyya, kamar da kasar Amurka, Birtaniya, Isara’ila da sauransu.

 

Sashe na 40, na kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 da aka sabunta, ya bai wa ‘yan kasar ikon haduwa a waje guda su kuma yi hudda da sauran jama’a.

 

Kazalika, sashe na 11 na yarjejeniyar nahiyar Afirka, da ke magana kan ‘yancin ‘bil’Adama, wanda ita kanta Nijeriya ta rattaba hannu kan wannan yarjejeniyar na barin ‘yan kasar su gudanar da zanga a cikin lumana.

 

Amma sai dai, abin takaicin duk da ‘yancin na wannan sashen, mahukunta Nijeriya, suna yawan take wannan ‘yancin, kan fakewa da cewa, suna tabbatar da bin doka da oda ne.

 

Misali, zanga-zangar #EndSARS, da ka yi a ranar 20 ga watan Okutobar 2020, da wasu matasan kasar suka gudanar a wasu titunan kasar, na a kawo karshen zaluncin da jami’an ‘yansanda ke yi, ta hanyar yakar masu yin fashi da makami da bukatar a inganta albashin ‘yansandan kasar, tare da kuma bukatar gwamnatin ta samar da wasu sauye-sauye.

 

Sai dai, zanga- zangar ta #EndSASR, da matasan suka gudanar a yankin Lekki ‘yansandan da aka tura zuwan wajen gudanar da zanga-zangar, sun rikidar da ita, ta zuwa nau’in yin amfani da Barkonon tsohuwa a kan masu zanga-zangar, wadda har suka yi amfani da bindigunsu, da ke dauke da Albarusai masu aiki, wajen bude wuta kan masu zanga-zangar, don su tarwatsa su, wanda har aka yi zargin, a lokacin, wasu masu zanga-zangar, sun rasa rayukansu.

 

Har zuwa yau, babu wani babban jami’in dansanda da aka dora laifin aikata wannan laifin, hasali ma, gwamnatin waccan lokacin, karyata wa ta yi, na cewa, an sanu rasa rai, a lokaci zanga-zangar.

 

Sai dai, sarkakiyar aukuwar wannan lamarin, abu ne, da har yanzu, ke ci gaba da zama a zuciyar alummar kasar.

 

Bayan korafe-korafen da suka biyo bayan aikata nau’in zaluncin na ‘yansanda, hakan ya tilasta gwamnatin waccan lokacin, rusa jami’n na #EndSARS.

 

Tun bayan rusa jami’an na #EndSARS, ‘yan Nijeriya sun yi tsammanin hukumomin tsaro, za su sauya takun su na kwantar da zanga-zangar lumana a cikin ruwan sanyi, amma har yanzu, hakan ba ta sauya Zani ba.

 

Babbban misali shi ne, zanga-zangar da wasu ‘yan Nijeriya suka yi a 2024, cikinsu har da kananan yara, na gwmnatin ta kawo karshen matsin tattalin arziki da, musamman talakwan kasar ke ci gaba da fuskanta, jami’an tsaro sun kama wsu su da dama tare da kuma tsare su a gidan Yari, bissa tuhumar su, da cin amanar kasa.

 

Sai dai, kiraye-kiraye suka yi yawa ne, gwamnatin ta ga uwar bari, ta janye tuhumar da cin amanar kasa ta kuma sako su.

 

Bugu da kari, zanga-zangar lumana a kwanan baya da Mista Omoyele Sowore,ya jagoranta wadda ake a turance, ake kira da ‘Take-it-Back Mobement’, a nan ma jami’an tsaro, sun tarwatsa ta hanyar yin amfani da Hayaki mai sanya Hawaye.

 

Wani abinda ke daure kai shi ne, a duk lokacin da masu zanga-zanga suka nuna goyon bayan wasu tsare-tsaren gwamnati, ba bu wani jami’in tsaro da ke auka masu.

 

Kazalika, wani lokacin gwamnati ta kan dauki nauyin wasu ‘yan bangar siyasa da ke gayon bayan ta, domin su aukawa masu zanga-zangar adawa da ita, koda kuwa, an tura jami’an tsaro wajen zanga-zangar, sai su burus su kyale, a ci zarafin su.

 

Irin wannan matakin na gwamnatin, ya nuna a zahiri, yazama na taka doka da oda da gwamnat ke yi, na tauye barin ‘yan kasar su fadi ra’ayinsu.

 

Sai dai, a lokacin tsohowar gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ta kasance ta bai wa ‘yan kasa damar yin zanga-zanga domin fadar ra’ayoyinsu, kan tsare-tsaren gwamnati, da suka ganin, ba su yi masu dadi ba.

 

Muna sane da rawar da Shugaban kasa mai ci, Ahmed Bola Tinubu, ya taka, kan zanga-zangar 2012, da a turance ake kira da ‘Occupy Nigeria’, da aka shafe mako daya ana gudar da ita, har ta kai ga ta janyo harkar kasuwanci ta tsaya cak a Legas, da sauran sassan Nijeriya, wadda manufarta shi ne, yaki da cire tallafin mai.

 

Hakazalika, tsohuwar minister Dakta Oby Ezekwesili ta jagoranci zanga-zangar ‘BringBackOurGirls’ (BBOG), inda suma wasu ‘yan Nijeriya, suka gudanar da irin wannan zanga-zangar, har ta kai tsawon kusa shekaru biyu a jere, ana guidanar da ita, domin su tilatawa gwamnatin ta kubutar da ‘yan matan na makarantar Chibok,

 

Zanga-zangar kwanan baya da miliyoyin Amukawa suka gudanar ta wadda kuma ta karade birane 1,000 na jihohi 50 na kasar, domin nuna adawarsu da tsare-tsaren gwamantin, ba bu wani jami’in tsaro da ya yi amfani da Albushi, ko Barkon tsohuwa kan masu zanga-zangar

 

Haka irin wannan batun yake a kasar In Isra’ila, musamman duba da zanga-zangar adawa ta kwana biyar da Isa’ilawa suka yi a 2023 kan sauye-sauyen da Faramintan kasar Benjamin Netanyahu, ya kirkiro da su a bangaren Shari’a, wanda gwamnatin ba ta matsawa masu zanga-zangar matuka ba, kuma ta tabbatar da an girmma ‘yancin masu gudanar da ita.

 

Abin tambayar a nan shi ne, mai ya sa a Nijeriya zanga-zangar lumana take komawa fagen jan daga a tsakanin masu gudanar da ita, da kuma jami’an tsaro?

 

Daya daga cikin amsar ita ce, salo ne kawai na gwamnati, na son tauyen hakkin ‘yan kasar, mai makon barinsu, su fadi ra’ayinsu.

 

Wannan dai, wani abu ne mai hadarin gaske, ba wai kawai na tauye masu hakkin ba, har da janyo Dimokirayya babban nakasu.

 

Dimkiradiyya ba wai kawai batun kada Kuri’a ba ne, amma akwai bukatar gwamnati, ta rinka sauraron ra’ayoyin ‘yan kasa, domin kuwa zanga-zangar lumana, na daya daga cikin bangaren da ‘yan kasa za su samu saurin isar da sakon su, ga gwamnati.

 

Wannan Jaridar na shawartar gwamnatin shugaba Tinubu, da ta bode kofar tattauna wa masu zanga-zangar lumana, daidai da tsarin Dimkaradiyya, mai makon yi masu barazana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: zanga zangar lumana masu zanga zangar jami an tsaro suka gudanar irin wannan

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta fara tantance ma’aikata don kawar da na bogi

Gwamnatin Jihar Gombe, ta fara aikin tantance ma’aikata sama da 7,000 ta hanyar Intanet domin tabbatar da bayanansu da kuma kawar da ma’aikatan bogi.

Shugabar Hukumar Kula da Ma’aikata ta Jihar (CSC), Hajiya Rabi Shu’aibu Jimeta, wacce ke jagorantar aikin, ta ce wannan shiri na nufin tabbatar da sahihancin bayanan ma’aikata.

An kashe mutum 2 a rikicin limancin masallacin Juma’a a Taraba An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a Anambra

Ta bayyana cewa za a kammala aikin cikin makonni takwas, kuma duk ma’aikatan da abin ya shafa za a ɗauki bayanansu domin sauƙaƙa samun bayanai.

Hajiya Jimeta, ta ce an keɓe ma’aikatan shari’a, hukumar malamai (Teachers Service Commission), da ma’aikatan lafiya, saboda hukumominsu na da tsarin tantancewa nasu.

Ta ƙara da cewa aikin na daga cikin shirin gyaran ma’aikata da gwamnatin jihar ke aiwatarwa domin gano ma’aikatan bogi da kuma waɗanda suka wuce lokacin ritaya.

“Bayan kammala aikin, za mu bai wa gwamnati shawara ta ɗauki sabbin ma’aikata da suka cancanta domin maye gurbin giɓin da ake da shi,” in ji ta.

A nasa jawabin, shugaban Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) reshen Gombe, Kwamared Yusuf Ash Bello, ya yaba da matakin.

Ya ce aikin na da muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya da inganta tsarin ma’aikata.

“Muna goyon bayan wannan aiki saboda zai samar da sahihin adadin ma’aikatan gwamnati. Ba za mu ci gaba da dogaro da bayanan bogi ko takardun bogi ba,” in ji Bello.

Wasu daga cikin ma’aikatan da aka riga aka tantance sun nuna farin cikinsu, inda suka bayyana cewa hakan zai taimaka wajen inganta hakkokinsu da ƙarin girma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • An sanya dokar hana fita bayan ɓarkewar zanga-zanga kan zaɓen Tanzania
  • Gwamnati ta bai wa ASUU N2.3bn domin biyan bashin albashin malamai
  • An saka dokar Ta Baci  Bayan Barkewar Zanga-zanga A Zaben Shugaban Kasar Tanzaniya
  • Gwamnatin Gombe ta fara tantance ma’aikata don kawar da na bogi
  • Senegal ta sake gano wasu shaidu kan kisan  gillar da aka yi a lokacin mulkin mallaka
  • Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi
  • An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa
  • Rikicin adawa da cin zaben Shugaba Paul Biya ya bazu a Kamaru
  • Jami’an tsaro sun harbi matar aure sun lakaɗa wa jama’a duka a Katsina