HausaTv:
2025-07-30@06:40:19 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya

Published: 25th, April 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan ‘wani makircin da kasar faransa ta kullawa falasdinawa a gaza’ don su amfana da kwararrunsu’ wanda ni tahir amin zan karanta.

///… Shugaba kungiyar kare hakkin bil’adama masi suna [the Euro-Mediterranean Human Rights Monitor] ta fallasa wani shiri tsakanin gwamnatin kasar faransa da HKI na fitar da kwararru da kuma masana falasdinawa da suka rage a Gaza, zuwa wajen yankin, kafin HKI ta fa wani gagarumin kissan kiyashi a yankin kashe falasdinawa da suka rage a yankin.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto Ramy Abdu shugaban kungiyar na fadar haka, ta kuma kara da cewa, offishin jakadancin kasar Faransa da ke birnin Qudus da aka mamaye, yana aiki tare da HKI don zakulo masana da kwararru a fannonin ilmi daban daban da ke tsare a cikin zirin gaza, zuwa wajen yankin saboda amfani da su don amfanin kansu.

Rahoton ya kara da cewa, wadanda zasu fitar daga yankin na Gaza, sun hada da dukkan masu digiri na uku wato PHD, likitoci, inginiyoyi, masanan tarihi da kuma wadanda suke da korewa a abubuwan al-adu da kayakin tarihi .

Kamfanin dillancin labaran Parstoday a kara da cewa wannan shi ne  wannan gagarumin aiki mikirce ne tsakanin Faransa da sojojin HKI na korar Falasdinawa daga Zirin gaza. Wannan shirin, inji Ramy Abdu ya sabawa dokokin kasa da kasa, kuma kasar faransa ta fada cikin wannan laifin wanda ake iya gurfanar da kasar da ta aikata haka a gaban kuliya.

Abdu ta kara da cewa abinda HKI ta kasa samu tare da amfani da makami tana son ta yi amfani da kungiyoyin kare hakkin bil’adama don cimma wanna manufar.

Kafar yada labarai da kasar Burtaniya mai suna ‘Middle East Eye’ HKI ta fara wani shiri na musamman, mai matakai 5 don tabbatar da ba wani bafalasdine da ya rage a Gaza, wanda kuma zai bata damar kafa kasar “yahudawa zalla’ a kan kasar Falasdinu.

Yahudawan sun sha nanata manufarsu ta ganin dukkan falasdinawa sun fice daga Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan tun bayan an fara yakin 7 ga watan Octpba shekara ta 2023.

Jaridar ta kara da cewa gwamnatin HKI ta fara aiwatar da wannan shirin, yana da matakai 5, kuma sun hada da, saka Falasdinawan cikin yunwa, rage yawan falasdinawa a gazar ta hanyar kashe su matukar iyawarsu, da lalata tsarin kiwon lafiya, ta yadda dan karamin cuta zata kashesu, maida gaza wurin da ba wanda zai ita rayuwa cikinsa,  sannan daga karshe anfani da dokokin kasa da kasa na maida gaza bangare na HKI bayan sun kammala kashe sauran falasdinawa a yankin.

Wannan ya nuna cewa zasu kashe falasdinawa kimani miliyon 2 a cikin karamin. Don haka a wannan tsarin suna ganin a mataki na 5 sun kammala kashe dukkan falasdinawa a gaza.

Jaridar ta kammala da cewa idan wannan shirin bai yi aiki ba suna da wani tsari wanda zai kasu ga shafe dukkan Falasdinawa a gaza. A cikin watan Jenerun wannan shekara ne shugaban kasar Amurka Donal trump ya bayyana wannan ra’ayin. Sai dai wannan ba ra’ayinsa na karan kansa ba, ra’ayi ne na yahudawan na samar da kasar yahudawa zalla tun asali.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: falasdinawa a gaza a kara da cewa

এছাড়াও পড়ুন:

An fara shigar da kayan agaji a Gaza

An fara shigar da kayyakin agaji zuwa Zirin Gaza wadanda galibi ta sararin samaniya aka rika jefawa da jirage daga kasashen Jordan da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Arshiyan Kohen, kakakin ma’aikatar tsaron Isra’ila ya ce, za a dakatar da farmakin soji na tsawon sa’o’i 10 a kowace rana a wasu sassan Gaza tare da ba da damar samun sabbin hanyoyin ba da agaji.

DW ya ruwaito cewa ana ci gaba danka kayayyakin tallafin a hannun kungiyoyin agaji na kasa da kasa da suke ci gaba da ayyukan rarrabasu.

Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Gutteress ya siffanta wannan matakin da mai sanyaya zuciya bayan damuwa da bala’in da mazauna Gaza suka tsinci kansu a ciki, yana mai fatar gaggauta shigar da kayayyakin agajin da kuma dorewarsa.

A yayin taron tattaunawa kan matsalolin da suke shafar ayyukan samar da abinci a Afrika ne Guterres ya faɗi  cewa yunwa ba za ta taɓa zama makamin da za a yi amfani da ita wajen yaƙi a duniya ba.

Babban jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher ya yi maraba da matakin, yana mai cewa yanzu haka yana tuntubar kungiyoyi wadanda za su yi duk mai yiwuwa don isa ga mutane da dama da ke fama da yunwa a wannan lokaci.

Tuni dai kungiyoyin agaji suka gabatar da wasu korafe-korafe tun ba a yi nisa ba, don yi wa tufkar hanci muddin ana son kwalliya ta biya kudin sabulu a ayyukan agajin da aka fara bayan fiye da watanni uku da dakatar da su.

Ahmad Nadir, na kungiyar lafiya ta duniya WHO, ya ce tsame hannun Isra’ila daga batun karba da rabon kayan agaji ne kadai zai bai wa kwarraru kan ayyukan agaji damar gudanar da ayyukan da za a samu nasara.

A bayan nan ne Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya WFP ta ce kashi uku na al’ummar Gaza ba su ci abinci na kwanaki ba, kuma mutane 470,000 suna cikin yanayi na juriyar tsananin yunwa wanda tuni ya kai ga mutuwar wasu.

Isra’ila dai na ci gaba da fuskantar suka daga kasashen duniya, kan amfani da yunwa a matsayin makamin yaki kan al’ummar Falasdinu, lamarin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da shi.

Akwai yunwa ta gaske a Gaza —Trump

Ko a wannan ɗin Litinin Shugaban Amurka Donald Trump ya ce “akwai yunwa ta gaske” a Gaza.

Shugaban na Amurka ya faɗi hakan ne bayan Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nace kan cewa babu yunwa a yankin.

Da aka tambaye shi ko ya yarda da abin da Netanyahu ya fada cewar “ƙarya ce tsagwaronta” idan aka ce Isra’ila na ta’azzara yunwa a Gaza, shugaban na Amurka ya ce: “Ban sani ba…amma yaran nan da ka gan su, suna cikin yunwa…wannan yunwa ce ta gaske.”

Kalaman Trump na zuwa ne bayan shugaban hukumar kai agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce ana buƙatar abinci mai “ɗimbin yawa” domin magance halin yunwa da yankin ke ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • HKI Ta ce Ta Tsaida Yaki A Gaza Na Wani Lokaci
  • VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?