HausaTv:
2025-09-17@23:08:58 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya

Published: 25th, April 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan ‘wani makircin da kasar faransa ta kullawa falasdinawa a gaza’ don su amfana da kwararrunsu’ wanda ni tahir amin zan karanta.

///… Shugaba kungiyar kare hakkin bil’adama masi suna [the Euro-Mediterranean Human Rights Monitor] ta fallasa wani shiri tsakanin gwamnatin kasar faransa da HKI na fitar da kwararru da kuma masana falasdinawa da suka rage a Gaza, zuwa wajen yankin, kafin HKI ta fa wani gagarumin kissan kiyashi a yankin kashe falasdinawa da suka rage a yankin.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto Ramy Abdu shugaban kungiyar na fadar haka, ta kuma kara da cewa, offishin jakadancin kasar Faransa da ke birnin Qudus da aka mamaye, yana aiki tare da HKI don zakulo masana da kwararru a fannonin ilmi daban daban da ke tsare a cikin zirin gaza, zuwa wajen yankin saboda amfani da su don amfanin kansu.

Rahoton ya kara da cewa, wadanda zasu fitar daga yankin na Gaza, sun hada da dukkan masu digiri na uku wato PHD, likitoci, inginiyoyi, masanan tarihi da kuma wadanda suke da korewa a abubuwan al-adu da kayakin tarihi .

Kamfanin dillancin labaran Parstoday a kara da cewa wannan shi ne  wannan gagarumin aiki mikirce ne tsakanin Faransa da sojojin HKI na korar Falasdinawa daga Zirin gaza. Wannan shirin, inji Ramy Abdu ya sabawa dokokin kasa da kasa, kuma kasar faransa ta fada cikin wannan laifin wanda ake iya gurfanar da kasar da ta aikata haka a gaban kuliya.

Abdu ta kara da cewa abinda HKI ta kasa samu tare da amfani da makami tana son ta yi amfani da kungiyoyin kare hakkin bil’adama don cimma wanna manufar.

Kafar yada labarai da kasar Burtaniya mai suna ‘Middle East Eye’ HKI ta fara wani shiri na musamman, mai matakai 5 don tabbatar da ba wani bafalasdine da ya rage a Gaza, wanda kuma zai bata damar kafa kasar “yahudawa zalla’ a kan kasar Falasdinu.

Yahudawan sun sha nanata manufarsu ta ganin dukkan falasdinawa sun fice daga Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan tun bayan an fara yakin 7 ga watan Octpba shekara ta 2023.

Jaridar ta kara da cewa gwamnatin HKI ta fara aiwatar da wannan shirin, yana da matakai 5, kuma sun hada da, saka Falasdinawan cikin yunwa, rage yawan falasdinawa a gazar ta hanyar kashe su matukar iyawarsu, da lalata tsarin kiwon lafiya, ta yadda dan karamin cuta zata kashesu, maida gaza wurin da ba wanda zai ita rayuwa cikinsa,  sannan daga karshe anfani da dokokin kasa da kasa na maida gaza bangare na HKI bayan sun kammala kashe sauran falasdinawa a yankin.

Wannan ya nuna cewa zasu kashe falasdinawa kimani miliyon 2 a cikin karamin. Don haka a wannan tsarin suna ganin a mataki na 5 sun kammala kashe dukkan falasdinawa a gaza.

Jaridar ta kammala da cewa idan wannan shirin bai yi aiki ba suna da wani tsari wanda zai kasu ga shafe dukkan Falasdinawa a gaza. A cikin watan Jenerun wannan shekara ne shugaban kasar Amurka Donal trump ya bayyana wannan ra’ayin. Sai dai wannan ba ra’ayinsa na karan kansa ba, ra’ayi ne na yahudawan na samar da kasar yahudawa zalla tun asali.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: falasdinawa a gaza a kara da cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.

Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.

Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000