Leadership News Hausa:
2025-10-31@16:32:20 GMT

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

Published: 31st, October 2025 GMT

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

Idan ka duba tarihin duniya gabadaya da tarihin annabawa, tarihi ne na wayewar duniya tun daga Annabi Nuhu (S.A.) har zuwa Manzon Allah (S.A.W.) kamar duniya tana ‘yar makaranta ce ta fara da Nazare, ta zo Firamare zuwa Sakandire har zuwa Jami’a, sannan aka yaye ta, yanzu da zuwan Manzon Allah an yaye duniya, yanzu duniya ba ta bukatar sai an aiko annabi, ba ta bukata sai an aiko ma’aiki, a’a wanna abu da Manzon Allah ya zo da shi za mu iya kafa dalili da shi mu shirya kanmu ba sai da annabi ba.

Wannan abu da Manzon Allah ya zo da shi yanzu ya kafa dalili da shi, da shi muka karantar da kanmu ba sai da Annabi ba, wannan abu da ya zo da shi za mu iya aiki da shi mu zauna lafiya, mu haramta abin da Allah Ya haramta. Yanzu kamar an yaye mu ne daga Jami’a tun daga jami’a tun daga zamanin Annabi Nuhu (A.S.) har ya zuwa Annabi Muhammadu (S.A.W.). idan ka faro duniya daga farkon ma’aika, duniya ta faro ne daga sanin wuta wato yadda za a yi amfani da wuta. Dan adam na farko ya ji tsoron wuta wasu sun tafi a kan cewa farkon abin da Dan Adam ya fara bautawa shine wuta, wanda ita ta fara ba shi tsoro ba wai ya iya kunnawa ba amma ya ga daki ya kama da wuta, dubi irin zamanin nan duk da motocin kashe gobara haka daji zai kama da wuta ta gagare su balle ka koma zamani da shekara miliyan kaza wanda dan Adam bai ma santa ba sai dai ya ga daki ya kama da wuta (wata ay ana cewa) “Allahn da ya sa muku wuta a ciki koren ganye ko koriyar bishiya”, malamai na cewa bishiya mai yado wanda ake kunna wuta, toh wannan abu ne ya sa idan wuta ta kama aka kasa shawo kanta sai mutane su tsorata su ce wai meye wannan, meye ya kunna wannan wutar? Suka ga to lallai wannan duniyar da suke ciki akwai wani abu a boye, gwara su bauta wa abin nan na boye fa, don ya kiyaye su daga wanna wutar har suka fara bauta mata da yanka dabbbobi don ta kiyaye su, gaba daya dai har ta soma gasa wasu abubuwa na dabbobi, idan wutar ta mutu suka zo wurin su ji kamshin ya bambanta, idan sun sa a baki su ji dadinsu ya banbanta. Toh tana daya daga cikin abin da ta koya wa dan Adam wayewa.

Da dan Adam ya waye, wuta tana daya daga cikin abin da ya wayar da dan Adam kuma idan ka lura yau wuta ita ke biye da mu duk wasu kere-kere za ka ga daga wuta ne, abin da muke tsoro kuma shi ne babban abin amfani, toh a haka dai dan Adam har ya iya kera wutar da kansa. Kamar yadda Allah ya fada mana cikin ‘ya’yan Adam da daya ya kashe daya ya rasa yadda zai yi, a haka ne har dan Adam ya san yadda zai binne dan’uwansa har zuwa zamanin Annabi Idirisu sama ta soma magana da kasa, Allah ya soma aiko ma dan Adam da mala’ika, su ne wadannan mutane da muke cewa ko akwai su a duniyar wata ko mutanen sama, Turawa duk sun rubuta wannan abu, sun zana wannan abu sai ga shi irin wannan jirage ne wanda ake cewa na duniyar sama, daya daga ciki Annabi Sha’ayahu yake cewa ga wani abu ya sauko kasa mai kara iri kaza.

Tun daga zamanin Annabi Idris mala’iku ne suka kawo sako suke yin magana da mutanen kasa, su ake cewa tatsuniyoyi na duk al’umma, tatsuniya ne a wajenmu amma su gaske ne a wajensu, su ce mutane sun sauko musu daga sama, har aka zo zamanin Annabi Nuhu ya tabbatar, da ya zo ya fada wa mutane suka ce ba su yarda ba, ba mu ji wannan wajen iyayenmu ba, haka aka ci gaba har zuwa zamanin Annabi Hudu dan Adam ya fara hore dabbobi, dabbar da dan Adam ya fara horewa shi ne kare, kuma ya hore dabbobin da zai ci, zai iya gane wannan dabbar ba zai ci ba wannan zai ci, wannan zai iya zama da ita lafiya, wannan ba zai iya zama da ita ba, daga nan dan Adam ya fara gini, ya dan kwakule kasa ya yi kogo ya shiga.

Har ya zuwa Annabi Salihu, har dan Adam ya fara fahimtar wannan kwayar da take fitowa a kasa, wannan zan iya ci in rayu, wannan kwayar kuma ba a cin ta, har ya soma tunanin toh wannan kwayar ya zan ajiye ta zuwa nan gaba in sake shuka ta, haka dan Adam har ya soma yin noma a aikace don ya rayu. Allah ya gaya mana wannan yana daga cikin ayoyin Allah (kamar yadda ya zo a aya) “arziki yana daga cikin kasa da abin da kasa take tsirarwa da abin da hannunka yake aikatawa” kamar sana’a ko noma ko nema. Toh ka ga a nan babu zancen ka ce ba za ka yi nema ba, duk abin da kake nema idan ka juya kasa za ka same shi, duka kasar da ta rike noma da sana’a za ku ga sun fi arziki, Allah ga shi ya gaya mana idan kafiri ya fi ka arziki sai dai ka nema a wajensa, don haka mu dogara da Allah shi ke azurtawa, ga ka’idoji nan ya fada mana, nema, kiwo abubuwa duk gabaki daya.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allahu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dan Adam ya fara

এছাড়াও পড়ুন:

Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher

Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi Allah wadai da harin da aka kai wa garin El-Fasher da ke Darfur a ranar Alhamis, da kuma mummunan tasirin da ya yi ga fararen hula.

A cikin sanarwar da ya fitar, kwamitin ya nuna matukar damuwarsa game da karuwar tashin hankalin da ke faruwa a El-Fasher da kewaye, wanda Rundunar Taimakon Gaggawa (RSF) ta kwace iko da shi kwanan nan, kuma ya yi Allah wadai da ta’addancin da ake zargin dakarun RSF sun yi wa fararen hula, ciki har da kisan gilla da tsare mutane ba bisa ka’ida ba.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce ta “firgita da rahotannin kisan sama da marasa lafiya 460 da abokan aikinsu a asibitin haihuwa na El-Fasher a Sudan.”

A cikin wani bidiyo da aka fitar a ranar Laraba a shafukan sada zumunta, Janar Hemedti ya amince cewa sojojinsa sun aikata cin zarafi.

Da yake magana daga wani wuri da ba a bayyana ba, janar din, sanye da kayan soja, cewa “Na lura da keta haddi a El-Fasher,” inda ya sanar da kafa kwamitin bincike nan take.

Ya yi alƙawarin cewa za a kama duk wani soja da aka samu da laifin cin zarafi kuma a gurfanar da shi a gaban kotu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya bukaci bangarorin da su hanzarta shiga tattaunawa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

kungiyar likitocin Sudan, ta ce “Adadin wadanda suka mutu ya wuce 2,000 a cikin kwanaki biyu na farko bayan da RSF ta shiga El-Fasher.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin  Faransa October 30, 2025  Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Amurka Ta Hana Marubuci Dan Nigeria Wole Soyinka Izinin Shiga Amurka October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna
  • Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15
  • An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin
  • An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna
  • DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya