Kare-karen Harajin Amurka “Dara Ta Ci Gida”
Published: 17th, April 2025 GMT
Bugu da kari, illar matakin na Amurka na iya gurgunta salon hada-hadar kudade, da kwadago, da kirkire-kirkire da kasuwannin kasa da kasa ke cin gajiyarsu.
Bisa la’akari da tarihi, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da banbance-banbance ta fuskar ci gaba, da yanayin gudanar masana’antu da karfin tafiyar da su, amma duk da haka ci gaban sassan biyu ya dunkule wuri guda, ta yadda illata sashe daya na iya haifar da koma baya ga dukkanin bangarorin biyu.
Ga misali, yayin da gwamnatin Amurka ke ta yayata manufar karin harajin ramuwar gayya, kamata ya yi mu lura cewa, Amurka na shigo da tarin hajoji da aka kammala sarrafawa, da wadanda ake kara sarrafawa a cikin kasar daga kasar Sin, matakin da ya yi matukar karfafa sashen masana’antun Amurka, ya kuma samarwa Amurkawa masu sayayya damar samun zabi na sayayya, da rahusar farashin abubuwan bukata na rayuwar yau da kullum, da karfafa ikon Amurkawa na sayen hajoji daban daban musamman ma masu matsakaici da karancin kudin shiga.
La’akari da hakan, za mu kara fahimtar cewa, ta hanyar hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka ne kadai manyan kamfanoni, da masana’antun Amurka za su iya kaiwa ga shiga a dama da su a fannin goyayya, da karfafa dunkulewar tattalin arzikinsu, sabanin yadda a yanzu Amurka ke yin matsin lamba, da kakaba haraji na cin zali, wanda zai gurgunta tattalin arzikin dukkanin sassa baki daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta
Kakakin hafsan hafsoshin sojojin Iran ya ce; Iran tana dora wa Amurka alhakin duk wani hari da za a kai mata
Kakakin hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Birgediya Janar Abul-fazl Shekarchi ya jaddada cewa: Iran tana dorawa Amurka alhakin duk wani harin wuce gona da iri da za a kaddamar kan kasarta.
A wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Mayadeen, Shekarchi ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran ba su ne suka kaddamar da harin kan wata kasa ba, amma sun mayar da martani cikin kwanaki 12 na arangama da munanan hare-hare da suka fuskanta daga mabartan ‘yan sahayoniyya makiya.
Ya kara da cewa, “An sanya wa makiya tsagaita bude wuta ne bayan da suka fuskanci munanan hare-hare daga sojojin Iran,” yana mai cewa, “Iran sakamakon karfin martanin sojojinta ne ta tilastawa makiya dakatar da yakin, ba kamar yadda suke ikirari ba, cewa su ne suka dakatar da yakin a kashin kansu, sannan kuma Iran ce karshen wacce ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka ciki kan mabarnata ‘yan sahayoniyya.”