Kare-karen Harajin Amurka “Dara Ta Ci Gida”
Published: 17th, April 2025 GMT
Bugu da kari, illar matakin na Amurka na iya gurgunta salon hada-hadar kudade, da kwadago, da kirkire-kirkire da kasuwannin kasa da kasa ke cin gajiyarsu.
Bisa la’akari da tarihi, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da banbance-banbance ta fuskar ci gaba, da yanayin gudanar masana’antu da karfin tafiyar da su, amma duk da haka ci gaban sassan biyu ya dunkule wuri guda, ta yadda illata sashe daya na iya haifar da koma baya ga dukkanin bangarorin biyu.
Ga misali, yayin da gwamnatin Amurka ke ta yayata manufar karin harajin ramuwar gayya, kamata ya yi mu lura cewa, Amurka na shigo da tarin hajoji da aka kammala sarrafawa, da wadanda ake kara sarrafawa a cikin kasar daga kasar Sin, matakin da ya yi matukar karfafa sashen masana’antun Amurka, ya kuma samarwa Amurkawa masu sayayya damar samun zabi na sayayya, da rahusar farashin abubuwan bukata na rayuwar yau da kullum, da karfafa ikon Amurkawa na sayen hajoji daban daban musamman ma masu matsakaici da karancin kudin shiga.
La’akari da hakan, za mu kara fahimtar cewa, ta hanyar hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka ne kadai manyan kamfanoni, da masana’antun Amurka za su iya kaiwa ga shiga a dama da su a fannin goyayya, da karfafa dunkulewar tattalin arzikinsu, sabanin yadda a yanzu Amurka ke yin matsin lamba, da kakaba haraji na cin zali, wanda zai gurgunta tattalin arzikin dukkanin sassa baki daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Kasarsa Ta Jajirce Kan Harkokin Diflomasiyya Domin Kare Hakkokinta
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Iran ta jajirce kan harkokin diflomasiyya kuma tana neman yarjejeniya ta gaskiya
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada kudurin kasar Iran kan harkokin diflomasiyya da kuma cimma daidaito bisa tsarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, tare da cikakken mutunta hakkin nukiliyar kasar Iran, da kuma tabbatar da manufar dage takunkuman da aka sanya mata.
Wannan dai ya zo ne a cikin jawabin da Araqchi ya gabatar a ranar Lahadin da ta gabata a wajen taron tattaunawa na birnin Tehran, wanda cibiyar nazarin harkokin siyasa da kasa da kasa ta ma’aikatar harkokin wajen kasar ta dauki nauyin shiryawa, tare da halartar tawagogi 200 na manyan jami’ai daga kasashe 53 da wakilan Majalisar Dinkin Duniya.
Yayin da yake yin bitar abubuwan da suka faru a shekarar da ta gabata kan fage na kasa da kasa da kuma manufofin ketare, Araqchi ya ce: “Abin takaici, shekarar da ta gabata na tattare da al’amura masu daci da kuma bala’in jin kai. Mafi yawan wadannan masifu su ne hare-hare da laifukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a Gaza, wadannan laifuffuka babu shakka za a iya daukarsu a matsayin bayyanannu kuma ba a taba ganin irinsu ba, ta hanyar watsa shirye-shiryen kisan kiyashi da aka yi a duniya a wani lokaci kuma ba a taba gani ba, ta hanyar watsa shirye-shiryen kisan kare dangi da aka yi a duniya. ko kuma a cikin fila-filan sararin samaniya.