HausaTv:
2025-12-04@05:32:25 GMT

WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka

Published: 17th, April 2025 GMT

Kungiyar kasuwanci ta duniya ta bayyana cewa, za a sami raguwar hajar da za a yi kasuwancinta a duniya  da kaso 0.2% saboda Karin kudin fito da Amurka ta yi.

Rahoton kungiyar kasuwancin ta duniya wanda aka fitar da shi a ranar Litinin din da ta gabata ta gina shi ne akan yadda tafiyar kasuwanci za ta kasance daga 2025-2026, wanda aka tsammaci zai rika samun bunkasa, sai dai kuma Karin kudaden fito da Donald Trump ya yi, ya sa kungiyar ta sauya hasashen da ta yi a baya.

Cinikayya ta kayayyaki zai ta yi baya da kaso 1.5% idan har Donald Trump din ya yi aiki da sabuwar siyasar tasa ta haraji.

Shugaban na Amurka ya dakatar da aiki da sabon salon haraji na tsawon kwanaki 90, domin bai wa kasashe 70 na duniya damar sauya yadda suke cinikayya da Amurka. Karin da Trump din ya yi wa kayan China ya kai kaso 145%, yayin da ya dan saukaka shi akan kasashen Canada da Mexico.

Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngozi Okonjo -Iweala ta sanar da cewa; Duk da cewa an sami tsaikon aiwatar da sabon haraji, amma duk da haka da akwai rashin tabbaci a kasuwannnin na duniya da hakan a kanshi yake a matsayin wani cikas na ci gaba.

Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar ta kasuwanci ta duniya tare da Asusun Bayar Da Lamuni su ka yi gargadi akan yadda za a sami koma baya a fagen kasuwanci da cinikayya a duniya ba, saboda matakin na kasar Amurka na Karin harajin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamasa Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza

Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar gwagwarmaya ta Hamas tayi tir da matakin da isra’ila ke dauka na tsauraran mataken shigar da kayan agaji zuwa yankin gaza musamman bangaren sansanin yan gudunn hijira da kuma tanti-tanti  da aka yi.

Kakakin kungiyar hamas Hazem Qaseem ya jaddada cewa mafakar da suka rage a yankin tantuna ne da aka yi marasa karko, da ba za su iya jurewa iska ko yanayin sanyi ba.

Yace har yanzu isra’ila tana bari a shiga da wani adadi kadan ne zuwa yankin gasa na kayayyakin agaji, wanda  ba zai wadatar da abubuwan bukatatun yau da kullum na rayuwa ba ga yawan alummar dake bukatar agaji a daidai lokacin da ake fuskantar mawuyacin yanayi dake bukatar taimakon gaggawa,

Qassem ya yi  kira ga masu shiga tsakanin da sauran kasashen duniya da su dauki mataken gaggawa kan isra’ila domin  ta bada damar shigar da kayayyakin agaji ga tantuna da aka yi kafin yanayin sanyi ya kara yin tsanani a yankin gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu. December 2, 2025 Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango December 2, 2025 Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau December 2, 2025 An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Don Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi December 2, 2025 Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma December 2, 2025 Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Kungiyar Hamasa Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza
  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar