HausaTv:
2025-12-15@03:06:13 GMT

WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka

Published: 17th, April 2025 GMT

Kungiyar kasuwanci ta duniya ta bayyana cewa, za a sami raguwar hajar da za a yi kasuwancinta a duniya  da kaso 0.2% saboda Karin kudin fito da Amurka ta yi.

Rahoton kungiyar kasuwancin ta duniya wanda aka fitar da shi a ranar Litinin din da ta gabata ta gina shi ne akan yadda tafiyar kasuwanci za ta kasance daga 2025-2026, wanda aka tsammaci zai rika samun bunkasa, sai dai kuma Karin kudaden fito da Donald Trump ya yi, ya sa kungiyar ta sauya hasashen da ta yi a baya.

Cinikayya ta kayayyaki zai ta yi baya da kaso 1.5% idan har Donald Trump din ya yi aiki da sabuwar siyasar tasa ta haraji.

Shugaban na Amurka ya dakatar da aiki da sabon salon haraji na tsawon kwanaki 90, domin bai wa kasashe 70 na duniya damar sauya yadda suke cinikayya da Amurka. Karin da Trump din ya yi wa kayan China ya kai kaso 145%, yayin da ya dan saukaka shi akan kasashen Canada da Mexico.

Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngozi Okonjo -Iweala ta sanar da cewa; Duk da cewa an sami tsaikon aiwatar da sabon haraji, amma duk da haka da akwai rashin tabbaci a kasuwannnin na duniya da hakan a kanshi yake a matsayin wani cikas na ci gaba.

Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar ta kasuwanci ta duniya tare da Asusun Bayar Da Lamuni su ka yi gargadi akan yadda za a sami koma baya a fagen kasuwanci da cinikayya a duniya ba, saboda matakin na kasar Amurka na Karin harajin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) a najeriya ta bayyana cewa za ta gudanar da zanga-zangar kasa baki ɗaya a ranar 17 ga Disamba, 2025, domin nuna damuwarta kan taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Wannan sanarwa ta fito ne daga sakon da NLC ta aikawa dukkanin majalisun jihohi a ranar 10 ga Disamba, bayan taron NEC da ta gudanar a ranar 4 ga watan. Kungiyar ta nuna damuwarta kan karuwar hare-haren ƴan bindiga  da satar mutane da ke ci gaba da addabar al’umma.

NLC ta mayar da hankali musamman kan sace ɗalibai mata a wata makarantar kwana da ke Jihar Kebbi a ranar 17 ga Nuwamba, inda ta bayyana mamaki cewa an janye jami’an tsaro daga makarantar kafin harin.

Ta ce wannan lamari ne mummunan kuma abin takaici da ya kamata a bincike shi sosai tare da gurfanar da duk masu hannu a ciki. Ƙungiyar ta zargi gwamnati da gaza daukar matakan da suka dace wajen kare rayukan dalibai a makarantu.

NLC ta ce dole ne gwamnati ta dauki mataki cikin gaggawa ta kammala bincike game da janye jami’an tsaro daga makarantar da aka kai harin, tare da ladabtar da masu laifi. A cewarta, rashin tsaron da ake fuskanta ya zama barazana ga rayuwa, da ilimi da ci gaban kasa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD)
  • َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci