HausaTv:
2025-11-19@10:07:43 GMT

WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka

Published: 17th, April 2025 GMT

Kungiyar kasuwanci ta duniya ta bayyana cewa, za a sami raguwar hajar da za a yi kasuwancinta a duniya  da kaso 0.2% saboda Karin kudin fito da Amurka ta yi.

Rahoton kungiyar kasuwancin ta duniya wanda aka fitar da shi a ranar Litinin din da ta gabata ta gina shi ne akan yadda tafiyar kasuwanci za ta kasance daga 2025-2026, wanda aka tsammaci zai rika samun bunkasa, sai dai kuma Karin kudaden fito da Donald Trump ya yi, ya sa kungiyar ta sauya hasashen da ta yi a baya.

Cinikayya ta kayayyaki zai ta yi baya da kaso 1.5% idan har Donald Trump din ya yi aiki da sabuwar siyasar tasa ta haraji.

Shugaban na Amurka ya dakatar da aiki da sabon salon haraji na tsawon kwanaki 90, domin bai wa kasashe 70 na duniya damar sauya yadda suke cinikayya da Amurka. Karin da Trump din ya yi wa kayan China ya kai kaso 145%, yayin da ya dan saukaka shi akan kasashen Canada da Mexico.

Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngozi Okonjo -Iweala ta sanar da cewa; Duk da cewa an sami tsaikon aiwatar da sabon haraji, amma duk da haka da akwai rashin tabbaci a kasuwannnin na duniya da hakan a kanshi yake a matsayin wani cikas na ci gaba.

Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar ta kasuwanci ta duniya tare da Asusun Bayar Da Lamuni su ka yi gargadi akan yadda za a sami koma baya a fagen kasuwanci da cinikayya a duniya ba, saboda matakin na kasar Amurka na Karin harajin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin tsaron MDD zai kada kuri’a kan daftarin kudirin Trump kan Gaza

A wani lokaci yau Litini ce kwamitin tsaro na MDD, zai kada kuri’a kan daftarin kudirin zaman lafiya na shugaban Amurka Donald Trump na Amurka kan Gaza.

Kafin hakan Amurka ta sha matsin lamba ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya don amincewa da daftarin kudurin na Trump.

Amurkar da wasu kawayenta na kasashen Larabawa sun yi kira ga Kwamitin Tsaron da ya “yi sauri” ya amince da daftarin kudurin wanda ya amince da shirin zaman lafiya na Donald Trump kan Gaza.

Qatar, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, Masar, Indonesia, Pakistan, Jordan, da Turkiyya sun bayyana goyon bayansu ga daftarin kudurin na Amurka wanda ya tanadi kafa kwamiti da zai kula da gwamnatin rikon kwarya a Gaza da rundunar kasa da kasa a yankin Falasdinu, tare da fatan amincewa da shi cikin sauri,” in ji su a cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa.

A ranar Alhamis, Amurka ta yi gargadi game da hadarin rashin amincewa da daftarin kudurin, Yayin da kasashen Larabawa ke nuna fargabar darewar yankin falasdinun gida biyu.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da wasu daga cikin ministocinsa sun sake nanata adawarsu ga kafa kasar Falasdinu kafin kada kuri’ar da za a yi yau Litinin kan daftarin kudurin kan Gaza, wanda ke nuna yiwuwar samar da kasar Falasdinu a nan gaba.

Kungiyoyin Falasdinawa sun yi watsi da daftarin kudurin wanda kuma ya tanadi shawarar tura dakarun kasashen waje kusan 20,000 zuwa Gaza, suna kira ga Aljeriya, wacce ba memba ce ta dindindin a kwamitin Tsaron, da ta yi watsi da shi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ansarullah Ta Yi Allah Wadai Da Sabunta Takunkumin MDD Kan Yemen November 17, 2025 Afirka ta Kudu na Binciken shigar wasu ‘yan gudun hijirar Falasdinu 153 cikin kasar November 17, 2025 Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo na biyu a jere November 17, 2025 DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23 November 16, 2025 An Yi Kira A Bai Wa ‘Yan Hijira Saboda Sauyin Muhalli Kariya November 16, 2025  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin November 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon November 16, 2025 Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025  Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila.   November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya za ta kara hannun jarinta a Amurka zuwa dala tiriliyan daya
  • Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
  • Brazil: Al’ummun Yankunan Karkara Na Amazon Sun Yi Gangami A Wurin Taron MDD Akan Muhalli
  • Afrika ta Kudu Ta yi Gargadi Game Da Duk Wani Yunkuri Na Fitar Da Falasdinawa Daga Yankin Gaza
  • Aref: Iran Tana Da Kyakkyawar Alaka Da Mambobin Kungiyar Hadin Gwiwa Ta Shanghai {SCO}
  • Kwamitin tsaron MDD zai kada kuri’a kan daftarin kudirin Trump kan Gaza
  • Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
  • DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23
  • An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
  • Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30