HausaTv:
2025-12-03@17:18:29 GMT

WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka

Published: 17th, April 2025 GMT

Kungiyar kasuwanci ta duniya ta bayyana cewa, za a sami raguwar hajar da za a yi kasuwancinta a duniya  da kaso 0.2% saboda Karin kudin fito da Amurka ta yi.

Rahoton kungiyar kasuwancin ta duniya wanda aka fitar da shi a ranar Litinin din da ta gabata ta gina shi ne akan yadda tafiyar kasuwanci za ta kasance daga 2025-2026, wanda aka tsammaci zai rika samun bunkasa, sai dai kuma Karin kudaden fito da Donald Trump ya yi, ya sa kungiyar ta sauya hasashen da ta yi a baya.

Cinikayya ta kayayyaki zai ta yi baya da kaso 1.5% idan har Donald Trump din ya yi aiki da sabuwar siyasar tasa ta haraji.

Shugaban na Amurka ya dakatar da aiki da sabon salon haraji na tsawon kwanaki 90, domin bai wa kasashe 70 na duniya damar sauya yadda suke cinikayya da Amurka. Karin da Trump din ya yi wa kayan China ya kai kaso 145%, yayin da ya dan saukaka shi akan kasashen Canada da Mexico.

Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngozi Okonjo -Iweala ta sanar da cewa; Duk da cewa an sami tsaikon aiwatar da sabon haraji, amma duk da haka da akwai rashin tabbaci a kasuwannnin na duniya da hakan a kanshi yake a matsayin wani cikas na ci gaba.

Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar ta kasuwanci ta duniya tare da Asusun Bayar Da Lamuni su ka yi gargadi akan yadda za a sami koma baya a fagen kasuwanci da cinikayya a duniya ba, saboda matakin na kasar Amurka na Karin harajin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma

A daidai lokacin ziyarar Paparoma Leo na XIV  shugaban Katolika na duniya a kasar Lebanon, kungiyar Hezbollah ta fitar da wata sanarwa a hukumance da aka aike masa.

Kungiyar ta yi maraba da ziyarar Paparoma, ta kuma jaddada muhimmancin Lebanon a matsayin kasa mai bambance-bambance na addini da kabilu da akidu, wadda al’ummominta suke bukatar rayuwa tare juna a cikin kwanciyar hankali da fahimtar juna a zamantakewa da siyasa.

A cikin wannan sakon, Hezbollah ta gabatar da Lebanon a matsayin gada wadda ta hada tsohon tarihi tsakanin Musulunci da Kiristanci da kuma tsakanin al’adu da akidu daban-daban.

Wasikar ta ambaci kalaman Paparoma John Paul II, wanda ya dauki Lebanon ba wai kawai a matsayin gida ba, a’a a ya dauki kasar ne a matsayin daya daga cikin wurare masu tasiri na addinai da aka saukar daga sama.

Hezbollah ta jaddada rawar da kasar ke takawa wajen samar da fahimta tsakanin addinai da al’adu. Wasikar ta nuna cewa rikicin duniya da ya samo asali daga rashin girmama hakkin dan adam, tare da hankoron bautar da shi da kuma tauye masa hakkokinsa, wanda kuma wannan Rashin adalcin ne ya share hanyar kaiwa zuwa ga tashe-tashen hankula da Rashin zaman lafiya a duk inda aka samu hakan.

Wani muhimmin bangare na wasikar ya yi ihara ne ga halin da ake ciki a Falasdinu. Hezbollah ta kira halin da ake ciki a Gaza da  “kisan kare dangi a fili” sannan kuma ta bayyana ayyukan Isra’ila a Lebanon shi ma a matsayin  “wani zalunci da ba za a yarda da shi ba,” kuma ta dauki wadannan matsalolin a matsayin sakamakon kwadayin gwamnatin Sihiyona na shimfida ikonta a  kan albarkatu da filaye na wadannan al’ummomi. Ta kuma jaddada cewa goyon bayan manyan ƙasashe ga Isra’ila a bayyane take haƙƙoƙin al’ummomin yankin ne.

Hizbullah ta kuma nanata alƙawarinta na kasancewa tare da gwamnatin dimokuraɗiyya mai zaman kanta, kiyaye tsaron cikin gida, da kuma fuskantar duk wani zalunci ko mamaye, kuma ta bayyana adawarta da tsoma bakin ƙasashen waje da ke barazana ga ‘yancin kai na Lebanon.

Wasikar ta kuma jaddada abubuwan da suka shafi Musulmai da Kiristoci, kuma ta bayyana mabiyan tafarkin Almasihu a matsayin manzannin zaman lafiya da kare haƙƙin ɗan adam.

Hizbullah ta yi kira ga Paparoma da ya ɗauki matsayi bayyananne wajen nuna Rashin amincwarsa da duk wani rashin adalci da zaluncin Isra’ila a lokacin ziyararsa a Lebanon, da kuma nuna haɗin kai da goyon ga al’ummar Lebanon.

Wasikar ta kammalawa da cewa,  Kungiyar Hizbullah na yin fatan alheri da fatan samun nasarar cimma burin tafiyar, na ganin an yada zaman lafiya da karfafa fahimtar juna tsakanin dukkanin Mabiya addinai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru   November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026