Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
Published: 13th, April 2025 GMT
Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.
Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance wajen asibiti.
Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.
Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.
Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da wani babban kwamiti kan kidayar jama’a da gidaje mai zuwa, inda ya umurci mambobin su gabatar da rahoton farko cikin makonni uku.
Shugaban wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa, Femi Gbajabiamila, a wajen taron da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja, ya ce kidayar na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasa da kuma tsare-tsare na gaskiya.
Ya lura cewa ingantaccen bayanan yawan jama’a yana da mahimmanci don yanke shawara mai inganci a cikin manyan sassan kamar kiwon lafiya, ilimi, tsaro, da kuma tsara tattalin arziki.
Shugaban ya jaddada cewa, an gudanar da kidayar jama’a ta karshe a shekarar 2006, wato kusan shekaru ashirin da suka wuce, kuma tun daga lokacin ne Najeriya ta fuskanci sauye-sauye a yawan al’umma, matsugunan jama’a, da kuma muhimman abubuwan da suka shafi kasa baki daya.
Ya kuma jaddada mahimmancin tsarin da aka yi amfani da shi na fasaha don tabbatar da sahihin sakamako mai inganci, inda ya bayyana bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin dukkanin hukumomin da abin ya shafa, da suka hada da hukumar kidaya ta kasa, da hukumar kula da shaida ta kasa NIMC, da ma’aikatar kudi, da ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare.
Shugaban kwamitin shugaban kasa kan kidayar jama’a da gidaje kuma ministan kasafin kudi da tsare-tsare, Sanata Atiku Bagudu, ya tabbatar da cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin wa’adin makonni uku da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar.
Bello Wakili/Abuja