HausaTv:
2025-07-13@06:35:55 GMT

Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari

Published: 13th, April 2025 GMT

Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.

 Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa  lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance  wajen asibiti.

Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.

Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.

 Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Eh, wasu mata suna daukar lambar motar duk wanda ya yi musu kyau ko ya zo da motar alfarma, su kai wa malami ko boka domin a janyo hankalinsa ya zo neman aurensu. Hakan kuskure ne babba, ba daidai ba ne a nemi aure ta hanyar sihiri ko dabara marar tsarki. Duk wata riba da ke tattare da hakan ba ta da karko, kuma tana iya dawo da akasin abin da aka nema, kamar rashin samun auren kwarai da tsayayye, zama da mutumin da ba da gaske yake ba, daukewar albarka daga rayuwa, fushin Allah da rushewar aure cikin lokaci. Shawara ga masu haka; ku dogara da addu’a, tarbiyya da hakuri, idan aure naku ne, zai zo da sauki cikin halal. Kada ku cuci kanku don burin duniya, ku tsaya akan gaskiya da dabi’a ta gari. A guji bin hanyar da ba ta dace ba domin cimma buri, duk mai hakuri sai ya ci riba.

 

Sunana Abba Abubakar Yakubu, Dan Jarida kuma Marubuci daga Jos:

Mata ku ji tsoron Allah, kuma ku nemi yardarsa

Innalillahi Wa Inna Ilaihir Raji’un! Wannan labari ne mai daga hankali da firgitarwa. Son auren miji mai kudi ko samun mijin aure mai rufin asiri ya rufe wa wasu mata ido, suna rasa imaninsu, don biye wa son zuciya. Lallai tsafi gaskiyar me shi ne, kuma abu ne mai yiwuwa a yi wa mutum asiri daga lambar waya ko wani abu mai nasaba da shi. Mutanen da suke shiga malamai don su jawo ra’ayin namiji da karfin asiri ba da addu’a ba, suna jefa kansu ne cikin tarkon shirka. Sannan ko da bukatar su ta biya ba lallai ne auren mutumin ya zama alheri ga rayuwarsu ba. Shawarata ita ce, duk abin da muke neman mallaka a rayuwarmu, mu yi addu’a mu nemi yardar Allah da zabinsa, domin idan Allah Ya kaddara za ki yi rayuwa da mutumin da kike so, zaman ya yi albarka, kuma ku ji dadin rayuwa da juna. Muna neman tsarin ubangiji daga sharrin malaman tsibbu, bokaye da matsafa dake rinjayar zuciyoyin mata marasa tsoron Allah. Su kuma masu yi Allah Ya shirye su. Amin

 

Sunana Balkisu Galadanchi Sokoto:

To da farko dai abin da zan ce shi ne; Ni ban yadda da boka ko malam ba, abin da kawai na sani kudirar Allah ce kadai za ta iya kawo wannan mutumin. Idan ya kasance motar ta aro ce kuma fa? Wannan babban kuskure ne, duba da cewar a Musulunci ma shirka ce, kuma tsaf za ki gayyato dan shan jini. Hakan sam ba riba, mugun kwadayi ne da zai iya janyo wa mutum halaka kai tsaye. Matsalolin da wannan abin zai iya haifarwa suna da dama musamman rashin tabbas, duk ranar da tsafi ya bar jikinsa da kan mutum zai yi bayani ai. Iyaye da ‘yan mata ku kama mutuncin kanku, ku sani hakan yi wa Allah shisshigi ne kuma shirka ce babba, Allah ta’ala ya sa mu dace.

 

Sunana Ibrahim Garba Bizi, Damaturu Jihar Yobe:

Wannan toshewar basira ce babba wanda mutum zai yi, ba ka san ta hanyar da ya samu motar ba, ko ta yankan kai ne ba ka sani ba. A’a kuskure ne gaskiya, ba ta da wani riba ko kadan a rayuwa. Zai Haifar da rashin imani, Allah ne ke azurtawa. Shawara su daina tun kafin mutuwa ta riske su saboda shirka ne, kar rayuwar duniya ta rude su, su nemi na kansu.

 

Sunana Princess Fatimah Mazadu daga Jihar Gomben Najeriya:

Subhanallahi Wa Azubillahi Minash-shaidanir Rajeem! cab-di-jam, wannan ai babbar shirka ce fakewa da aure ta hanyar yaudara da tilastawa, kuma mafi kuna ta sabon Allah ba ta hanyar addu’ar; ubangiji ya hadaka da naka rabon ba, ko da bai kai wanda ka gani din ba, Allah ya kiyaye mana imanin mu. Eh! gaskiya ana yi saboda mata da yawa suna fariya sun auri mazajensu ta wannan hanyar ‘more especially’ akan ‘plat forms’ na Instagram, snap chat, tiktok da sauransu, gaskiya ana yi duk da ni na fi yarda don Allah ne ya bar su da dabararsu. Abu ne mara kyau a zahiri da badini, babu wata riba ko kadan sai tarin nadama da da-na-sani, ‘yes’ ka cika burinka ka auri abin da ka ke so ta karfi, amma kwanciyar hankali fah? babu shi don Allah shi ke azurtawa kuma ke ba da duk wani abu da bawa ke nema da bukata kan ya roke shi ma. Akwai matsaloli masu tarin yawa, kamar rasa Imani, taurin zuciya, buri da kwadayi, da-na-sani da zubar mutunci ranar da duk asiri ya tonu, asara biyu ga mari ga tsinka jaka, biyu babu, ba mutunci, babu masoyin. Saboda duk tsayi da tasirin asiri ba ya ‘lasting’ wata rana abin zai warware a bazata ke kare shekarun duniyar ki kina nadama ke da iyayen naki. Mata ko tsoro ba sa yi don ka kansa da mota ka san halayensa ne? watakila dan yawo ne, ko dan daba, ko mazinaci, ko mashayin giya, wanda jurarsa zai rika baki wahala, kin ga farin ciki ya zamo bakin ciki.

 

Sunana Labaran Jibrin Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Batu na farko hakan na nuna san zuciya karara a fili kenan, sai kuma ta fuskar addini hakan babban kuskure ne, domin rashin bar wa Allah zabi akan abu mafi alkhairi. Kuma mene ne hukunci mai duba taurari a Musulunci? Saboda haka duba taurari ai kamar bugun kasa ne, dame bugun kasa da wanda ake bugawa mu kalli hukuncin su a addinance. Abu na biyu babu wata riba ga mai hankali, kuma ko hausawa kan ce kowa ya hau motar kwadayi ya zama dole a sauke shi a tashar wulakanci. Abu na uku dole akwai matsaloli sosai domin ba za ma mu ce matsala ba misali kin ga mutum da babbar mota ba bincike shin wane ne shi ya halayyarsa kuma mece ce sana’arsa da sauransu, daga karshe ma wata kila ‘yahoo boys’ ne ko wani matsafi ko kawali da dai sauransu daga ranar da asirin hakan ya tashi tun a nan duniya riba aka ci ko faduwa, ba a zo kan maganar addini ba ma, shin mai duba taurari da kuma wanda za a duba masa haram za su ci ko halak, Manzon Allah (S.A.W). ya ce ku ciyar da iyalanku da halal, kuma ku shayar da kanku da iyalanku da halal, domin duk naman jikin dan’adam din da aka gina da halal ko wuta ba ta bukatar ci.

 

Sunana Fatima Nura Kila, A Jihar Jigawa:

Tabbas mu kan ji wannan labarin mu ma, amma zahiri akwai wadanda suke aikata wannnan dabi’ar kuma wasu su kan yi nasara, amma wasu su kan yi akasin haka. Tabbas babban kuskure ne a Musulunci ma, babu wata riba a ciki domin a karshe su kan yi da-na-sani, abin da yake janyo wa hakan kuma san duniya ne, da kuma dole wasu matan sai sun auri masu kudi saboda a ganinsu auren me kudi shi ne jin dadi bayan ba haka ba ne. Zai haifar da matsaloli wacce sai a gaba mace za ta gane abin da ta aikata babban laifi ne. Shawarar da zan bawa masu wannnan akida su sani duk inda arzikinka yake tabbas zai zo kawai lokaci ne, amma sun kasa ganewa, fatan mu Allah ya sa mu fi karfin zuciyar mu.

 

Sunana Khadija Auwal Koki, A Jihar Kano:

To gaskiya wannan babban kuskure ne ya kamata iyaye da ‘ya’yan su ji tsoran Allah, domin aure lokaci ne kuma su san hakan babbar illa ce, domin kuwa ba su san wanda za su janyo ba, watakila ya zame musu da-na-sani. Hakan ba, abu ne mai kyau ba, domin kuwa iyaye za su jefa ‘ya’yansu ne a kan turbar da-na-sani, kuma hakan ba zai haifar da da mai ido ba. kuma kwadayi ke jawo haka, kuma an ce kwadayi mabudin wahala. Hakan na iya janjo hulakanci da rashin ganin mutuncin juna da kuma rashin zaman lafiya, domin soyayyar ba ta Allah da Annabi ba ce. Shawara ita ce duk mai hali irin wannan ya yi gaggawar sauya halinsa kuma ya tuba ya mika lamarinsa zuwa ga Allah.

 

Sunana Hussy Saniey, daga Jihar Katsina:

Mutane sun zama abin da suka zama, sun mayar da kwadayi sana’arsu, shi ya sa har suka dauki wannan hanyar suke ganin ita ce mai billewa a gare su tare da taimakon wani mushirikin da ke irin wannan aikin. Za a iya dacewa domin an ce tsafi gaskiyar mai shi amma idan har mai motan ya rike azkar da hannu bibbiyu to ba za su ci nasara akan shi ba. Wannan abin babban kuskure ne suke aikatawa kuma babu wata riba da za su samu sai dai ma su tsinci larabarsu a talatarsu, domin za su janzo wa kansu nadama marar amfani. Babbar matsala kuwa hakan yake janyowa domin shi asiri tasirinsa na lokaci kadan ne daga ya karye kuma yarinya za ta tsinci kanta a duniyar zawarci bayan imaninta da ya raunana. Shawara ita ce su yi hakuri su daina suna zaune Ubangiji zai kawo masu namijin da yake daidai da rayuwarsu, wanda zai rike su fiye ma da yadda suke hari domin Allah ya fi su sanin abin da ya dace da rayuwarsu.

 

Sunana Hafsat Sa’eed daga Naija:

Yin hakan kuskure ne, domin ba a san me za a daukowa kai ba, dan shaye-shaye ne, ko dan daba ne, ko matsafi, ko me wata mummunar dabi’ar da ba a so, wanda zai addabi al’umma kuma a je a haifi ‘ya’ya cikin rashin sa’a a haifo me dabi’unsa, ya kamata a kula da irin wadannan abubuwa dan wannan sam! ba ci gaba bane, ci baya ne aka samu a daina kallon abubuwa komai ya zama wayewa ko zamani ana yi masa kallon ci gaba, a roki Allah zabi mafi alkhairi.

 

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor), Jihar Kano:

Gaskiya wannan abu bai dace ba sam! an kauce hanyar addini kuma an kama hanyar bata. Wai mai muke son zama ya Allah, babban burin mace ta yi addu’ar samun miji nagari ba mai kudi ba. sai ki ga Allah ya bar mutum da aniyarsa an samu mai kudin karshe a kare a wahala, Allah ya kyauta. Yo ai abu ne a bude babu wani kyau ko alfannu sai bata da tabewa, sannan abin duniya na wasu iyayen dan ba duka aka taru aka zama daya ba, Allah dai ya yi mana magani. Aure da aka gina shi da soyayya da kauna ma yanzu ya Allah ya cika bale auren asiri da zarar ya karye shikenan an tsinci kai a tashar wulakanci. Abin da zan ce Allah ya kyauta ya yi mana magani ya shiryi masu yi su gane gaskiya kawai.

 

Sunana Aisha Lawan Ya’u Momy, Jihar Kano Ado Bayero Layout:

Tabbas hakan yana faruwa ga wasu marasa ilimi, kuma sai an yi shirka sannan hakan ke tabbata. Kuma wannan ba abu ne me kyau ba, kwadayi da hangen wanda suka fika shi ke janyo hakan. Babbar matsalar sai ya tabbata an yi aure zama ya yi zama sannan za a fuskanci wulakanci saboda ba a gina shi akan sunna ba. Shawara ga masu aikata hakan su yi hakuri wallahi duk yadda ki ke mijinki yana nan ubangiji ya zaba miki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra\ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa A Zirin Gaza
  • Jamhuriyar Nijar Da China Sun Kusa Warware Sabanin Dake Tsakaninsu Akan Batun Man Fetur
  •   Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i Kadan
  • Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • An Kashe Jami’in Sojan HKI A Gaza
  • An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran