Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
Published: 13th, April 2025 GMT
Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.
Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance wajen asibiti.
Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.
Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.
Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe
Ƙungiyar Agaji ta Red Cross ta Najeriya (NRCS), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Italiya, ta kafa cibiyoyin Rage Haɗurran Bala’o’i (Disaster Risk Reduction – DRR) a makarantun sakandare guda biyu a Jihar Gombe, domin inganta shirye-shiryen kare kai daga bala’o’i da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin matasa.
Makarantun da suka amfana da wannan shiri su ne Ƙaramar Sakandaren Gwamnati ta Pilot da kuma Sakandaren Gwamnati ta Comprehensive, Deba.
NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a KanoA yayin bikin ƙaddamar da cibiyoyin, ƙungiyar Red Cross ta raba kayan karatu da suka haɗa da jakunkuna masu ɗauke da bayanai kan DRR, littattafan rubutu, alƙalumma da kayan lissafi ga dalibai, domin ƙara musu ilimi da shiri na kare kai daga haɗurra.
Sakataren Red Cross reshen Jihar Gombe, Murtala Aji Alliyu, ya bayyana cewa manufar wannan shiri ita ce “kama su tun suna ƙanana,” ta hanyar koya musu ilimi mai amfani a fannoni huɗu — wato tsaftar muhalli, bayar da agajin gaggawa, yada bayanai, da kuma shirye-shiryen kare kai daga bala’o’i.
Ya ce ana aiwatar da wannan shiri a jihohi 12 na Najeriya domin rage haɗarin bala’o’i da kuma ƙarfafa tsaron al’umma ta hanyar ilmantar da matasa tun daga makaranta.
“Manufar ita ce a shirya matasa su san yadda za su kare kansu da kuma yadda za su amsa idan wata gaggawa ta faru. Idan aka ba su ilimi, za su zama jakadun sauyi da za su taimaka wajen gina al’umma mai juriya da tsaro,” in ji Alliyu.
A nasa jawabin, wanda ya wakilci Sarkin Deba, Alhaji (Dr) Ahmad Usman, wato Hakimin Bokna, Alhaji Abubakar Usman Tafidan Deba, ya yaba wa Red Cross da Gwamnatin Italiya bisa wannan shiri da ya bayyana a matsayin mai matuƙar amfani.
Ya buƙaci dalibai su ɗauki shirin da muhimmanci tare da haɗa gwiwa da malamansu domin tabbatar da ɗorewarsa.
Mataimakiyar Shugabar Makarantar Gwamnati ta Pilot, Malama Salifatu Abubakar, wacce ta wakilci shugaban makarantar, ta gode wa Red Cross bisa wannan kyakkyawan aiki, tare da kira ga ɗalibai da su yi amfani da ilimin da aka koya musu yadda ya kamata.
Ta ce wannan shiri ba wai ɗaliban kawai zai amfanar ba, har ma zai taimaka wajen yaɗa ilimin kare kai daga bala’o’i da kuma tabbatar da tsaro a faɗin Jihar Gombe.
Wasu daga cikin malamai da ɗalibai sun nuna farin ciki da wannan shiri, inda suka bayyana shi a matsayin abin da ya zo a kan kari kuma mai tasiri sosai.
Sun kuma yi kira ga sauran ƙungiyoyin agaji da na ci gaba da su yi koyi da Red Cross wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su taimaka wajen gina al’umma mai juriya da kwanciyar hankali.