HausaTv:
2025-04-18@23:03:39 GMT

Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata

Published: 13th, April 2025 GMT

 Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ” Amnesty International”  ta bayyana cewa, rundunar kai daukin gaggawa ta “RSF” ta bautar da mata da kuma cin zarafinsu.

Kungiyar ta yi tir da abinda rundunar ta “RSF” ta yi akan mata da su ka manyanta da kuma ‘yan mata a tsawon lokacin yakin na Sudan da har yanzu bai zo karshe ba.

Wani sashe na rahoton kungiyar ya yi ishara da yadda wannan rundunar da take fada da sojojin kasar Sudan ta tarwatsa mutane daga gidaje da matsugunansu a fadin kasar.

Ita kuwa Hukumar dake kula da ‘yan gudun hijira ta MDD ( UNHCR) cewa ta yi da akwai yan kasar ta Sudan fiye da 100,000 da suke neman yin hijira zuwa kasashen turai a cikin wannan shekara ta 2025 kadai, tare da kara da cewa mutanen suna kara yanke kauna da samun wata mafita a cikin kasar, saboda raguwar agaji.

A cikin birnin Khartum da sojojin su ka kori dakarun na “RSF” an sami komawar mutanen da su ka yi hijira kamar yadda hukumar ta ( UNHCR) ta ambata.

 Shugabar hukumar mai kula da ‘yan hijira ta MDD Olga Sarado wace ta gudanar da taron manema labaru a birnin Geneva ta bayyana cewa; Da akwai ‘yan Sudan su 484 da su ka isa cikin kasashen turai daga watan Janairu zuwa yanzu, da hakan yake nuni da samun Karin masu hijirar zuwa turai da kaso38%.

Ta kuma kara da cewa, matukar ba a kai wa kasar kayan agaji, to kuma masu yin hijira zuwa turai din zai karu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Gombe, Bello Yahaya ya bayar da umarnin tura isassun jami’ai a fadin jihar domin samar da isasshen tsaro kafin bukin Easter, da kuma bayan bikin Easter.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar a Gombe.

 

A cewarsa, an tura jami’an dabarun dakile hare-hare zuwa muhimman wuraren da suka hada da wuraren ibada, wuraren shakatawa, kasuwanni, da sauran wuraren taruwar jama’a.

 

Ya kuma ce, kungiyoyin sintiri da jami’an tsaron cikin za su kasance a kasa domin sanya ido kan ayyukan da kuma gaggauta daukar matakin magance duk wata matsala idan ta taso.

 

Kwamishinan ya lura cewa rundunar tana aiki tare da hadin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma domin kula da su a cikin doka da oda yayin da ake ƙarfafa ‘yan ƙasa su kasance masu bin doka da oda kuma su kai rahoton duk wani abin da ake tuhuma ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

HUDU/GOMBE

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Matar gwamna ta ɗauki nauyin ragon suna da hidimar duk matar da ta haifi ’yan uku a Sakkwato
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Tsohon Minista Ya Zargi Isra’ila Da Kasashen Yammacin Turai Da Kitsa Kashe-kashen Rayuka A Nijeriya 
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • An Gudanar Da Taron Kasa da Kasa Don Tallafawa Yan Gudun Hijirar A Sudan