HausaTv:
2025-12-10@14:19:21 GMT

Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata

Published: 13th, April 2025 GMT

 Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ” Amnesty International”  ta bayyana cewa, rundunar kai daukin gaggawa ta “RSF” ta bautar da mata da kuma cin zarafinsu.

Kungiyar ta yi tir da abinda rundunar ta “RSF” ta yi akan mata da su ka manyanta da kuma ‘yan mata a tsawon lokacin yakin na Sudan da har yanzu bai zo karshe ba.

Wani sashe na rahoton kungiyar ya yi ishara da yadda wannan rundunar da take fada da sojojin kasar Sudan ta tarwatsa mutane daga gidaje da matsugunansu a fadin kasar.

Ita kuwa Hukumar dake kula da ‘yan gudun hijira ta MDD ( UNHCR) cewa ta yi da akwai yan kasar ta Sudan fiye da 100,000 da suke neman yin hijira zuwa kasashen turai a cikin wannan shekara ta 2025 kadai, tare da kara da cewa mutanen suna kara yanke kauna da samun wata mafita a cikin kasar, saboda raguwar agaji.

A cikin birnin Khartum da sojojin su ka kori dakarun na “RSF” an sami komawar mutanen da su ka yi hijira kamar yadda hukumar ta ( UNHCR) ta ambata.

 Shugabar hukumar mai kula da ‘yan hijira ta MDD Olga Sarado wace ta gudanar da taron manema labaru a birnin Geneva ta bayyana cewa; Da akwai ‘yan Sudan su 484 da su ka isa cikin kasashen turai daga watan Janairu zuwa yanzu, da hakan yake nuni da samun Karin masu hijirar zuwa turai da kaso38%.

Ta kuma kara da cewa, matukar ba a kai wa kasar kayan agaji, to kuma masu yin hijira zuwa turai din zai karu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta

Mai Magana da yawun fadar mulkin Rasha Dmitry Viskov ya ce; Fadar mulkin kasar tana maraba da matakin da shugaban kasar Amurka ya dauka na bitar siyasar tsaron kasar, da ta kunshi cire kasar Rasha a matsayin barazanar da Amurkan take fuskanta.

Viskov ya fada wa kamfanin dillancin labarun “Tass” cewa; a cikin sabon tsarin tsaron kasar ta Amurka an cire Rasha a matsayin baraza, don haka yana kira da a samo hanyoyin aiki tare akan muhimman batutuwa na duniya.

Haka nan kuma ya ce; Wannan matakin ci gaba ne sosai.

Wannan sabuwar siyasar tsaron ta Amurka tana yi wa China a matsayin babban kalubale ta fuskar tattalin arziki, don hakan Amurka za ta yi aiki domin sake dawo da adalci da kuma abinda ta kira ‘yancin Amurka.”

Sai dai kuma ta jaddada wajabcin ci gaba da jibge sojoji a yankin tekunan Inida da kuma Pacific domin abinda ta ce kokarin hana afkuwar yaki.

Haka nan kuma ya bayyana fatansa na ganin sabuwar siyasar tsaron Amurka ta share fagen kawo karshen yakin kasar Ukirniya da kuma tattaunawa da bude sabuwar alaka da Amurka, da hakan shi ne ra’ayin shugaba Vladmir Putin.

Matakin na Amurka akan Rasha ya bakantawa kasashen turai da suke son Amurkan ta zamar musu jagora a yakin da suke yi da Rasha ta hanyar kasar Ukiraniya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan
  • Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato