Aminiya:
2025-12-10@05:27:23 GMT

Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum

Published: 25th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa a harkar tsaron sararin samaniya, domin hana ’yan ta’adda na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare.

Zulum, ya faɗi haka ne a ranar Juma’a a garin Mafa, bayan wani hari da Boko Haram suka kai.

Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam

Ya ce, “Babban abin da nake son magana a kai shi ne amfani da jirage marasa matuƙa.

An shaida min cewa sun yi amfani da su a Dikwa, kuma hakan abu ne mai tayar da hankali.”

Gwamnan ya bayyana cewa yawaitar irin waɗannan jirage a hannun mahara barazana ce ga tsaron ƙasa.

“Dole mu haɗa kai domin magance wannan sabon salo,” in ji shi.

Zulum, ya kuma nemi a ƙara tsaurara tsaro a bakin iyakoki da kuma inganta tsaron sararin samaniya.

A cewarsa: “Wannan abu ne da ya kamata a yi cikin gaggawa, ba tare da ɓata lokaci ba.”

Haka kuma, ya yi kira ga jama’ar jihar da su bai wa jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar kai musu bayanan sirri da za su taimaka wajen magance matsalolin tsaro.

Ya ƙara da cewa: “Mun samu labari cewa za a kai hari a Mafa, kuma mun sanar da hukumomin da ya kamata su sani. Amma ganin yadda abubuwa suka faru, akwai alamun zagon ƙasa, don haka ya kamata a bincika a kuma yi gyara.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Jirage Marasa Matuƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin

Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.

Fadar gwammnatin faransa ta Élysée ta ce bisa bukatar hukumomin Benin ta bayar da “goyon baya ta fuskar bayar da bayanai da dabaru” ga sojojin Benin a matsayin martani ga yunkurin juyin mulki da aka dakile a karshen makon da ya gabata.

Sanarwar ta ce Emmanuel Macron ya yi hadin gwiwa” da “musayar bayanai da kasashen yankin,” in ji daya daga cikin masu ba shi shawara ga manema labarai, a cewar AFP.

Shugaban Faransa ya yi magana a ranar Lahadi da takwaransa na Benin, Patrice Talon, wanda sojoji suka nemi su hambarar, da kuma shugaban Najeriya da kuma kasar Saliyo.

Kasar Saliyo ce ke rike da shugabancin kungiyar ECOWAS, wacce ta dauki matakin soja don taimakawa Cotonou wajen dakile yunkurin juyin mulki.

Dama a jiya Shugaban Bola Tinubu ya tabbatar da cewa sojojin kasarsa sun taimaka wajen dakile juyin mulki a benin.

Wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaban ya fitar ta ambato Shugaba Tinubu yana cewa “sojojin sun mayar da martani wajen ceto dimokuraɗiyya ta 35.”

Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya dauki mataki bayan samun buƙatar neman ɗauki daga Benin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda December 9, 2025  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba