Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello
Published: 25th, October 2025 GMT
Aƙidar Dr Bello abu ne mai saƙin gaske kuma akwai hikima a ciki sosai. Shi ne kuma samar da ingantacciyar kiwon lafiya wand aba wai sai kana da kuɗi mai yawa ba.
Tsarinsa shi ne haɗa yi wa mutane aiki, ilimantar da su tared fda kuma tsugunar da su. Wannan mataki ne da yake tabbatar da an samun cikin gaggawa da kuma sauƙin gaske.
Daga Legas zuwa Kano, daga Ondo zuwa Kuros Riba, kungiyar CFDF tana tafiya da kayan aiki na tafi da gidanka da kuma rundunar likitoci masu tiyata na sa kai, masu aikin jinya, da ma’aikatan jinya. Kowace manufa asibiti ce mai motsi – duba marasa lafiya, yin hadaddun tiyata, da bayar da shawarwari da tallafin abinci mai gina jiki ga iyalai waɗanda a da suna tunanin warkarwa ba ta isa ba.
A ƙarƙashin shugabancinsa, gidauniyar ta zama wani samfur na yadda za a gudanar da samar wa da al’umma kiwon lafiya mai sauƙi kuma mai inganci, musamman tiyata a fuska.
Canza Tsari Ba Canza Fuska kawai Ba
Cutar Cleft lips da palates sun daɗe suna takura wa al’umma. Yara na kunyar fita cikin mutane, ana kuma tsangwamar iyaye mata da iyalai inda ake ɗora musu lafin aukuwar cutar.
Ayyukan Dr Bello suna kula da waɗannan yanayi n acuta, ana kuma amfani da tiyatar da ake yi wajen yaƙar jahilci. Duk gangamin da aka ana amfani da shi wajen faɗakar da al’umma akan ainihin yadda cutar take tare da kuma ƙarfafa wa al’umma kawo mara lafira domin amagani a kan lokaci.
Ta hanyar ilimantar da al’umma da kuma bibiyar mara lafiya bayan an yi masa tiyata a yanzu an samu rage tsoro da jin kunya a zukatan mutane, mutane kuma na ƙara fahimtar cewa, wannna cut aba tsinuwa ba ne abu ne da za a iya warkar da shi ta hanyar kimiyya da fasaha.
Likitan Tiyata, Masani kuma bawan Allah
Cikakken masani kuma ƙwararren likitan tiyata a a babban asibitin fadar shugaban ƙasa, Dr Bello yana shugabanci cikin matsuwa da hangen nesa.
Mamba ne na ƙungiyoyi da dama da suka haɗa da ‘National Postgraduate Medical College of Nigeria (FMCDS), West African College of Surgeons (FWACS), International Congress of Oral Implantologists (FICOI) da kuma Global Congress of Implantology (FGCOI).
A mastayoinsa na malamai, Dr Bello ya karantar tare da sa ido a ayyukan matasan likitoci masu tasowa da dama, ta haka za a tabbatar da sun gaji irin ƙwarewarsa tare da samar wa al’umma fata na gari.
Ya kuma rubuta muƙaloli na kimiyya fiye da 35 ya kuma ƙirƙiro ‘International Craniofacial Academy (ICA) a Abuja, ya kuma ci gaba da yi wa mutane tiyata kyauta ba tare da ko sisi ba.
Abin Ya Fi Batun Ɗakin Tiyata
A wajen asibitin, Dr Bello yana da alaƙa da tushen sa. Yana riƙe da matsayin Aare musulmi na Ago Are, shugaban kungiyar ci gaban Oke Ogun (reshen Abuja), kuma ya shahara dawajen yi wa al’umma hidima.
Amma ga marasa lafiyarsa, “likita ne kawai mai sanya murmushi ga fuskan al’umma.”
Samar da Kiwon Lafiya Mai Dorewa
A shekarar 2010 aka kafa gidauniyar “ Cleft and Facial Deformity Foundation” an kuma gudanar da tiyata sama da 50 a duk yankuna shida na ƙasar nan.
Misalin haɗin gwiwarsa tare da gwamnatocin jihohi, asibitocin koyarwa, da al’ummomin gida ya tabbatar da cewa ingantaccen tsarin kiwon lafiya yana buƙatar ingantattun ababen more rayuwa.
Alƙalumma Basa Ƙarya
An yi tiyata 2,600 kyauta, An kammala ayyukan jinya 50 a faɗin Nijeriya
Ɗaruruwan ma’aikatan lafiya sun sami horo a yankunan karkara
Dubban iyalai ne aka faɗakar a kan rashin fahimtasu ga yadda cutar take.
Rayuwar Da Ke Taimakawa Motsi
Dr Bello ya zaburar da masu aikin sa kai a Yammacin Afirka don yin hidima ga marasa lafiyata hanyar daidaita tsakanin manufofi da aiki, ya nuna cewa ƙudurin likitan fiɗa ɗaya zai iya zama matakin samun nasara ga kiwon lafiyar al’umma.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Shekarar 2025 kiwon lafiya Dr Bello ya
এছাড়াও পড়ুন:
ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.
ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.
Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.
Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.
Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.
Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.
A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.
Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”
ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.
Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.
Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.