Aminiya:
2025-12-10@09:18:58 GMT

Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki

Published: 25th, October 2025 GMT

Rundunar Sojin Najeriya za ta fuskanci babban sauyi wanda zai tilasta wa manyan sojoji yin ritaya daga aikinsu.

Rahotanni sun bayyana cewar akalla Janar-Janar 60 ne ake sa ran za su yi ritaya sakamakon sabbin sauye-sauye da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Hafsoshin Tsaro.

’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC

Sanarwar da aka fitar a ranar Juma’a ta tabbatar da sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaro tare da wasu hafsoshi.

Janar Laftanar Olufemi Oluyede, wanda a baya shi ne Babban Hafsan Sojin Kasa, shi ne yanzu sabon Babban Hafsan Tsaro.

Janar Meja Waidi Shaibu shi ne sabon Babban Hafsan Sojin Kasa, yayin da Air Vice Marshal Sunday Kelvin Aneke, ya zama sabon Babban Hafsan Rundunar Sojin Sama.

Hakazalika, Rear Admiral Idi Abbas, ya zama Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, yayin da Janar Meja E.A.P. Undiendeye ya ci gaba da rike mukaminsa na Babban Hafsan Rundunar Leken Asiri ta Tsaro.

Majiyoyi daga rundunar soji, sun bayyana cewa wannan sauyi zai yi sanadin ajiye aikin manyan jami’an da suka fi sabbin hafsoshin matsayi, kamar yadda tsarin aikin soji ya tanada.

Wata majiya ta ce: “Da zarar an rantsar da sabbin hafsoshin, wadanda da suka fi su matsayi za su yi ritaya.”

Rahotanni sun ce jami’an da abin zai shafa sun fito ne daga tawagar da suka yi kwas na 38, 39 da kuma wasu daga tawaga ta 40 na Makarantar Horon Sojoji ta NDA.

A cewar majiyoyi, yana cikin tsarin aikin soji na tabbatar da ladabi, bin doka, da kiyaye tsarin mulki na rundunar.

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa an dauki matakin ne domin inganta harkar tsaro da kuma inganta hadin kai tsakanin bangarorin rundunonin tsaro.

Sabbin nade-naden na zuwa ne kwanaki kadan bayan jita-jitar yunkurin yin juyin mulki da ta karade kafafen yada labarai.

Sai dai babu wata hujja da ta nuna cewa wadannan rahotanni na da nasaba da sabbin nade-naden.

Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa yi wa manyan jami’ai ritaya zai bai wa sabbin kwamandoji matasa damar su jagoranci rundunonin tsaro, lamarin da ka iya kawo sabon sauyi a harkar tsaro.

Tsohon mai magana da yawun rundunar sojin kasa, Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka (mai ritaya), ya bayyana cewa matakin da aka dauka abu ne da aka saba gani a tsarin aikin soja.

A cewarsa, sauyin shugabanci kan kawo sabbin dabarun aiki.

A wata sanarwa da hadimin shugaban kasa, Sunday Dare, ya fitar, fadar shugaban kasa ta yaba wa tsofaffin hafsoshin bisa sadaukarwarsu da kishin kasa, inda ta bayyana cewa sabbin nade-naden na daga cikin kokarin gwamnatin Tinubu na inganta tsarin tsaron kasa da tabbatar da zaman lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rundunar Sojin Najeriya Sabbin Hafsoshin Tsaro Tsaro Rundunar Sojin bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki

A jiya Talata ne dai aka zartar da hukuncin kisa akan wani babban jami’in Banki na gwamnati bayan da aka same shi da laifin barnata dukiya.

Kafafen watsa labarun kasar China sun ce mutumin da aka zartarwa da hukuncin kisan, tsohon manaja ne a wani babban kamfani na hukuma.

A shekarar 2024 ne dai  aka sami Bay Tian Hua, saboda samunsa da karbar toshiyar baki da ta kai dalar Amurka miliyan 156 domin bai wa wani kamfani fifiko samun kwangilar aiki a tsakanin 2014-2018.

Tashar talabijin din CCTV ta gwamnatin kasar China ta ce; kotun al’umma ce ta yanke hukuncin akan wannan laifin da ta bayyana da cewa mai matukar hatsari ne.

An zartar da hukuncin kisan ne dai akan  Bay a garin Tianjin dake yankin arewa maso gabashin kasar, bayan da ya yi bankwana da ‘yan’uwansa.

A kasar China dai ana zartar da hukuncin kisa akan wadanda aka samu dacin hanci da rashawa. Wasu lokutan kuma ana rage hukuncin kisan zuwa zaman kurkuku na shekaru biyu, ko kuma zaman kurkuku na har abada.

Kamfani da Bay ya yi wa manaja yana cikin manyan cibiyoyin kudi na bayar da bashi mai rassa a fadin kasar ta China.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila