Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki
Published: 25th, October 2025 GMT
Rundunar Sojin Najeriya za ta fuskanci babban sauyi wanda zai tilasta wa manyan sojoji yin ritaya daga aikinsu.
Rahotanni sun bayyana cewar akalla Janar-Janar 60 ne ake sa ran za su yi ritaya sakamakon sabbin sauye-sauye da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Hafsoshin Tsaro.
’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADCSanarwar da aka fitar a ranar Juma’a ta tabbatar da sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaro tare da wasu hafsoshi.
Janar Laftanar Olufemi Oluyede, wanda a baya shi ne Babban Hafsan Sojin Kasa, shi ne yanzu sabon Babban Hafsan Tsaro.
Janar Meja Waidi Shaibu shi ne sabon Babban Hafsan Sojin Kasa, yayin da Air Vice Marshal Sunday Kelvin Aneke, ya zama sabon Babban Hafsan Rundunar Sojin Sama.
Hakazalika, Rear Admiral Idi Abbas, ya zama Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, yayin da Janar Meja E.A.P. Undiendeye ya ci gaba da rike mukaminsa na Babban Hafsan Rundunar Leken Asiri ta Tsaro.
Majiyoyi daga rundunar soji, sun bayyana cewa wannan sauyi zai yi sanadin ajiye aikin manyan jami’an da suka fi sabbin hafsoshin matsayi, kamar yadda tsarin aikin soji ya tanada.
Wata majiya ta ce: “Da zarar an rantsar da sabbin hafsoshin, wadanda da suka fi su matsayi za su yi ritaya.”
Rahotanni sun ce jami’an da abin zai shafa sun fito ne daga tawagar da suka yi kwas na 38, 39 da kuma wasu daga tawaga ta 40 na Makarantar Horon Sojoji ta NDA.
A cewar majiyoyi, yana cikin tsarin aikin soji na tabbatar da ladabi, bin doka, da kiyaye tsarin mulki na rundunar.
Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa an dauki matakin ne domin inganta harkar tsaro da kuma inganta hadin kai tsakanin bangarorin rundunonin tsaro.
Sabbin nade-naden na zuwa ne kwanaki kadan bayan jita-jitar yunkurin yin juyin mulki da ta karade kafafen yada labarai.
Sai dai babu wata hujja da ta nuna cewa wadannan rahotanni na da nasaba da sabbin nade-naden.
Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa yi wa manyan jami’ai ritaya zai bai wa sabbin kwamandoji matasa damar su jagoranci rundunonin tsaro, lamarin da ka iya kawo sabon sauyi a harkar tsaro.
Tsohon mai magana da yawun rundunar sojin kasa, Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka (mai ritaya), ya bayyana cewa matakin da aka dauka abu ne da aka saba gani a tsarin aikin soja.
A cewarsa, sauyin shugabanci kan kawo sabbin dabarun aiki.
A wata sanarwa da hadimin shugaban kasa, Sunday Dare, ya fitar, fadar shugaban kasa ta yaba wa tsofaffin hafsoshin bisa sadaukarwarsu da kishin kasa, inda ta bayyana cewa sabbin nade-naden na daga cikin kokarin gwamnatin Tinubu na inganta tsarin tsaron kasa da tabbatar da zaman lafiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rundunar Sojin Najeriya Sabbin Hafsoshin Tsaro Tsaro Rundunar Sojin bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal.
Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.
A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta.
Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura tare da samar da kayan aiki na zamani. Haka kuma an gyara tare da samar da kayan aiki ga babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Kauran Namoda a jihar. Babban asibitin da ke Kauran Namoda da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da shi, an samar da kayan aiki don isar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya yadda ya kamata. Kazalika, an sanya na’urorin bincike, gadaje, injinan ECG, injin centrifuge, injinan gwaje-gwajen jini, na’urar tantance jini ta atomatik da sauran wasu kayan aiki.
Kazalika, an kuma inganta babban asibitin Nasarawar Burkullu da ke Ƙaramar Hukumar Bukkuyum. Bayan ayyukan kiwon lafiya da suka haɗa da na gaggawa, aikin tiyata, kula da lafiyar mata da yara, tsarin wurin keɓewa, wurin ajiyar gawa, ɗakunan tiyata na maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, shagon magani, kula da mata masu juna biyu da kula da yar, duk an gina su. Sauran gyare-gyaren, sun haɗa da shingen gudanarwa, wuraren ma’aikata, masallatai da rijiyoyin burtsatse.
Haka kuma, a Ƙaramar Hukumar Maru, an gyara babban asibitin tare da samar da kayan aiki na zamani.
Gwamnan ya kuma kaƙƙamar da aikin sabunta birane, wanda ya kai ga gyara manyan tituna a jihar.
Dangane da batun tsaro kuwa, a shekarun baya-bayan nan, Zamfara ta ɗan samu jinkiri. A wannan lokaci na Gwamna Lawal, kashe-kashe da garkuwa da mutane ya ragu matuƙa a jihar. Hakan ya biyo bayan kafa jami’an tsaron da aka kafa a dukkanin kananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.
An horar da mutanen da aka zaɓo a tsanake, bisa cikakkiyar kulawar jami’an tsaron hukumar DSS, sannan suna yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro na yau da kullum, domin yaƙi da ‘yan fashi a jihar. A kwanakin baya ne gwamnan ya raba motocin aiki guda 140 da aka ware wa ƙungiyoyin tsaro daban-daban a faɗin jihar.
An haifi Dauda Lawal Dare, a ranar 2 ga Satumbar 1965, a Jihar Zamfara. Bayan kammala karatunsa na Firamare da Sakandare, ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa. Ya kuma yi digirinsa na biyu (M.Sc) a fannin kimiyyar siyasa/Hukunce-hukuncen ƙasa da ƙasa duk a jami’ar. Ya ƙara da digirin-digirgir (PhD) a fannin harkokin kasuwanci a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.
Bayan kammala karatunsa na digiri na uku, ya yi kwasa-kwasai a Makarantar Kasuwanci ta Harɓard, Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Oɗford, Makarantar Tattalin Arziƙi ta Landan, Makarantar Kasuwancin Legas da sauransu.
Gwamnan ya yi aiki a matsayin jami’in ilimin siyasa tare da MAMSER, hukumar wayar da kan jama’a, don tabbatar da adalci da dogaro da kai a Nijeriya. A 1989, ya shiga Westeɗ Nigeria Limited a matsayin mataimakin babban manaja.
An naɗa shi a matsayin mataimakin ƙaramin jami’in shige da fice (immigration), a shekarar 1994, sannan ya zama babban jami’in hulɗa da jama’a a ofishin Jakadancin Nijeriya, Washington, DC, Amurka.
A shekarar 2003, ya koma bankin First Bank, a matsayin manajan hulɗa da jama’a, kuma a lokuta daban-daban ya kasance babban manaja a ofishin Abuja. A shekarar 2011, ya samu muƙamin mataimakin shugaban zartaswa, sashen gwamnati na Arewa na bankin na First Bank, bayan ya yi ayyuka da dama. A shekarar 2012, Dauda Lawal ya zama babban darakta a sashen gwamnati na Arewa, na First Bank.
Daga baya ya shiga siyasa ya kuma tsaya takarar Gwamnan Jihar Zamfara. A zaɓen fidda gwani na APC da aka gudanar a shekarar 2018, ya sha kaye a hannun Idris Shehu Mukhtar. A zaben Gwamnan Jihar Zamfara na 2023, ya tsaya takara; kuma ya yi nasara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA