Matawalle Ya Bada Tallafin Kudi Da Kayayyakin Abinci Ga Iyalan Marigayi Sarkin Gusau
Published: 28th, July 2025 GMT
Ministan Harkokin Tsaron Ƙasa, Dakta Bello Mohammed Matawalle, ya baiwa iyalan marigayi Sarkin Gusau, Alhaji Ibrahim Bello, gudummawar naira miliyan biyar da kuma kayan abinci, bayan rasuwarsa a ranar Alhamis da ta gabata a birnin Abuja sakamakon gajeruwar rashin lafiya.
Dakta Matawalle, ya bayyana alhininsa bisa wannan rashi na Mai Martaba.
Baya ga gudummawar kuɗi, ministan ya kuma bada buhunan shinkafa 20, gero 10, masara 10 da kuma dawa 10 ga iyalan mamacin.
Wata tawaga mai ƙarƙashin jagorancin Sanata Hassan Muhammad Nasiha, tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara a zamanin mulkin Matawalle ne suka miƙa gudummawar a madadin ministan.
Dakta Matawalle ya bayyana marigayi Sarkin Gusau a matsayin shugaba mai ɗabi’a ta gari, wanda ya kasance mai sauƙin kai da tausayi a duk tsawon mulkinsa.
Ya ambato irin jajircewarsa wajen kula da marayu da taimaka musu wajen samun ilimi, inda da dama daga cikinsu suka zama mutane masu amfani a cikin al’umma.
“Rasuwar Sarkin ta bar gibidmai wuyar cika,” in ji Matawalle, yana mai addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, tare da baiwa iyalan haƙurin jure rashin.
Da yake karɓar tawagar da gudummawar a madadin iyalan, Hakimin Sunami, Alhaji Mainasara Bello Ciroman Gusau, ya nuna godiya ga ministan bisa wannan gudummawar.
Ya ce masarautar za ta ci gaba da tunawa tare da girmama goyon bayan da Matawalle ke baiwa masarautu, musamman a lokacin da yake gwamna.
Tawagar ta haɗa da fitattun mutane irinsu Ibrahim Umar Dangaladima, Sakataren APC na Jiha; Bashir Idris Ataka, Sakataren Walwala na APC; Mallam Yusuf Idris Gusau, Sakataren Yaɗa Labarai na APC; Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, Mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa, da sauransu.
Haka kuma, Sheikh Tukur Sani Jangebe ya yi addu’ar Allah ya ji ƙan marigayi Sarkin Gusau.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Matawalle Zamfara Sarkin Gusau
এছাড়াও পড়ুন:
Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu A Kaduna
Ƙungiyar Rotary Club ta Kaduna Metropolitan ta raba kayan haihuwa fiye da 70 ga mata masu juna biyu a cibiyar kiwon lafiya ta Mando, Afaka.
Da yake jawabi a wajen taron, shugaban Rotary Club na Kaduna Metropolitan kuma shugaban Rotary Action Group for Peace, Rotarian Luqman Babatunde, ya jaddada cewa kayan haihuwar ba na siyarwa ba ne, kyauta ce don tallafa wa mata masu juna biyu musamman marasa ƙarfi.
Ya ce wannan tallafin ana gudanar da shi ne a wurare daban-daban a jihar Kaduna, yana mai jaddada cewa gwamnati kaɗai ba za ta iya yin komai ba, shi ya sa ake buƙatar goyon bayan ƙungiyoyin sa-kai da na taimakon jama’a irin su Rotary.
Ya bayyana cewa wannan shirin ya samu ne ta haɗin gwiwa da kamfanin MotherCat, wanda ke kusa da cibiyar lafiya, don tunawa da watan kula da lafiyar uwa da jarirai.
Ya shawarci matan da su yi amfani da kayan yadda ya kamata tare da tunatar da su taken Rotary, Service Above Self, yana mai ƙarfafa su su rika taimaka wa wasu idan dama ta samu.
Shi ma ya sake jan hankalin masu cin gajiyar su yi amfani da kayan cikin hikima.
Haka nan, gwamnan yankin Rotary Clubs, Rotarian Joy Okoro, wanda Rotarian Victor Majekodunmi ya wakilta, ya bayyana cewa mata da dama masu juna biyu waɗanda ba su da ƙarfin siyan kayan haihuwa kan haifi jarirai a gida cikin mawuyacin hali.
Ya jaddada cewa wannan kyauta ba ta gwamnati bace, an samo ta ne daga gudummawar kungiyoyi da mutane masu kishin jinƙai, yana mai roƙon matan su yi amfani da kayan yadda ya dace.
Ita kuma babban jinya ta cibiyar lafiya, Hajiya Murjanatu Ahmed Rabiu, ta koka kan yadda wasu mata masu juna biyu ke ɓoye kayan haihuwar da gwamnati ko kungiyoyin ci gaban al’umma suka ba su, domin su karɓi kuɗi daga mazajensu.
Ta yi gargadin cewa su daina wannan dabi’a, tana mai cewa an rubuta sunaye da lambobin wayar waɗanda suka amfana a yau, kuma idan ya zama dole za a sanar da mazajensu cewa matansu sun karɓi kayan haihuwa kyauta daga Rotary.
A sakon ta na musamman, shugabar Ƙungiyar Matan ‘Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ), Comrade Sahura Jibrin Maidoki, ta roƙi matan masu juna biyu su nuna kayan haihuwar ga mazajensu domin rage musu nauyin kuɗi da kuma bawa mazajen damar mayar da hankali kan wasu bukatu. Ta kuma yi gargadin cewa kada su sayar da magunguna da sauran kayan tsaftar da ke cikin kyautar.
Mata biyu da suka amfana, Salamatu Tijjani da Faith Tori, sun gode wa Rotary da abokan haɗin gwiwarta saboda kyautar, suka kuma yi alkawarin yin amfani da kayan yadda ya kamata.
Wasu daga cikin kayan da aka raba sun haɗa da magungunan mata masu juna biyu, jakunkuna, kayan tsafta, ‘pads’, da ‘diapers’ da sauransu.
Wannan shirin, wanda ya yi daidai da Watan Lafiyar Uwa da Jarirai na Rotary International, ya samu halartar shugaban Rotary Club na Kaduna Main, Rotarian Ahmad Tijjani, da sauran shugabannin ƙungiyar a Kaduna tare da abokan haɗin gwiwa ciki har da Mothercat da NAWOJ.
COV: Naomi Anzaku Ekele