Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir
Published: 28th, July 2025 GMT
Al’ummar Arewacin Najeriya na shirin kayar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 saboda ƙuncin rayuwa da kuma tsare-tsaren gwamnatinsa da suka mayar da yankin saniyar ware.
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ne ya bayyana haka, yana mai cewa gamayyar shugabanni da ’yan siyasar Arewa na haɗa ƙarfi da ƙarfe domin tsayar Da ɗan takara da nufin yaƙar gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027.
Babachir David Lawal ya bayya cewa shugabannin siyasar Arewa na aiki tare da Kungiyar Kare Muradun Arewa (ACF) da Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) domin cin ma wannan manufa, kuma “Babu yadda za a yi mutum ya ci zaɓe na tare da samun goyon bayan waɗannan ƙungiyoyin ba.”
Ya ƙara da cewa tsare-tsaren Tinubu ciki har da cire tallafin mai da tsadar rayuwa sun jefa ’yan Najeriya cikin matsanancin rayuwa, don haka shugabannin siyasar Arewa ke ƙoƙarin fito da ɗan takararsu a zaɓen da ke tafe.
Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a NejaYa bayyana haka ne a yayin wata tattaunawa da shi aka yi a tashar Talabijin ta Trust TV, inda ya bayyana cewa.
A cewarsa, “Maimakon saukaka wa al’umma halin da suke ciki, sai wannan gwamnati ta ɓige da ƙirƙiro abubuwan da ke ƙara jefa ’yan Najeriya cikin tsanani. Saboda haka dole a tsayar da ita.”
Game da muƙaman da Tinubu ya yi nada ’yan Arewa a baya-bayan nan, wanda ake tunanin ya yi ne domin lallashin yankin, Babachir ya bayyana naɗe-naɗen a matsayin shafe-shafe.
Ya ce, “Ni ne na fata yaƙar takarar Musulmi da Musulmi a wancan lokacin. Yanzu kuma da na ga ya naɗa Kirista a matsayin Shugaban Jam’iyya, na shan Musulmi zai ƙara ɗauka a matsayin mataimakinsa.”
Ya yi zargin Tinubu ya yi naɗe-naɗen ne domin ya raba kan masu zaɓe, “Amma Musulmin da suka zaɓe shi ma ya yi watsi da su, ya kawo musu koma baya, ya mayar da su saniyar ware.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Kayar da Tinubu Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.