An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
Published: 28th, July 2025 GMT
An gano gwawar mutum 15 a yayin da ake ci gaba neman wasu uku bayan hastarin kwalekwale da ya auku a yankin Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja.
Kwalekwalen ya kife ne a yayin da yake ɗauke da mutum 43 da buhuna 60 na shansherar shinkafa da shanu uku da tumaki biyu a ranar Asabar.
Kifewar kwalekwalen ta auku ne a sakamakon karonsa da wani kututture bayan ya ɗauki fasinjojin daga yankin Guni zai kai su kasuwar mako-mako da ke yankin Zumba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro.
Manajan Hukumar Albarkatun Koguna ta Ƙasa (NIWA), mai kula da yankin, Akapo Adeboye, ya ce an gano gwawar mutum 15, amma ana ci gaba neman wasu mutum uku, ko da yake cewa an yi nasarar ceto mutum 26 da ke sanye da rigunan kariya da ransu, bayan aukuwar hatsarin.
HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INECAdebayo ya bayyana cewa, “Mutanen sun taso ne daga ƙauyen Shayita za su tafi Kasuwar Kwata da ke Zumba tare da kayansu na miliyoyin kuɗaɗe a ranar Asabar 26 ga watan Yuli, 2025.
“Jami’an NIWA sun gudanar da aikin ceto, amma an samu asarar rayuka 18, an ceto wasu 26, kuma aka ci gaba da aiki da kuma ƙoƙarin kamo mai kwalekwalen.”
Shaidu sun ce hastarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Asabar, kuma yawancin fasinjojin mata ne da ƙananan yara, kuma jami’an Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) sun tabbatar da hakan.
Sarkin Ruwan Zumba, Umar Isah, ya ce mutum 15 ne suka rasu, an ceto 25, amma an yi asarar shanu uku da buhu 60 na shansherar shinkafa.
“A cikin mutum 15 da suka rasu har da ƙananan yara uku mata da gano gawarwakinsu,” in ji shi.
Amma Darakta Janar na Hukumar NSEMA, Abdullahi Baba Arah, ya ce gawa 13 aka gano kuma an yi jana’izarsu a ranar Lahadi.
Arah, wanda ya tabbatar da asarar wasu mutane da dabbobi da kayan abinci a hatsarin, ya ce gawarwakin sun haɗa da mata takwas da maza uku da kuma yara biyu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari Jirgin ruwa kwalekwale
এছাড়াও পড়ুন:
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
A yayin da ‘yan sandan ke gudanar da bincike a yankin, rahotanni sun ce jami’an sun gano wata mata ‘yar Nijeriya a Coach A-2, Seat No. 27, tare da wani yaro da wata jakar balaguro kala-kala.
Rahoton ya bayyana cewa bayan an yi mata tambayoyi, ta bayyana sunanta Doris daga Nijeriya kuma ta ce yaron da ke tare da ita, wanda ta bayyana sunansa Miracle, nata ne.
RPF ta lura cewa “da aka yi mata tambayoyi a gaban shaidu masu zaman kansu, matar ta amsa cewa tana dauke da kayan maye.”
Daga baya an kai ta zuwa gidan RPF a Panbel domin cikakken bincike.
Rahoton ya lura cewa a cikin jakar balaguron, jami’an sun gano bakaken fakiti guda biyu da aka lullube da kayan roba da aka yi wa lakabi da “BINTAGE.”
A cewar ‘yansanda, na’urorin gwajin muggan kwayoyi daga baya sun tabbatar da cewa abin da ke ciki hodar iblis ce mai nauyin kilogiram 2.002.
Binciken da aka yi a baya ya gano wata jakar Mickey Mouse mai ja-da-shudi ta yara da ta boye a cikin babbar jakar.
‘Yansandan sun bayyana cewa karamar jakar na dauke da fakitin takardu guda biyu – daya mai lakabin “Kellogg’s Corn Flakes” da sauran “Bongchi Perfect Roll.”
An samu rahoton cewa wadannan suna dauke da fararen sinadarai na crystalline, daga baya aka gano su da methamphetamine, mai nauyin kilogiram 1.488.
Hukumomin CR sun tabbatar da cewa “magungunan da aka kama, darajarsu ta kai kusan Rs 36 crore”
Etumudon ta zama mace ta biyu ‘yar Nijeriya da aka kama a Indiya cikin kasa da watanni biyu bisa laifin safarar muggan kwayoyi.
Ta bi sahun wasu ‘yan Nijeriya da dama da a halin yanzu ke fuskantar shari’a a kasar kan irin wadannan laifuka.
“Aikin da aka gudanar cikin bayanan sirri, an kaddamar da shi ne da hadin gwiwa kuma an gudanar da bincike a kan isowar jirgin a Platform No. 7, Panbel Railway Station,” in ji jami’an CR.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp