Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
Published: 28th, July 2025 GMT
Wani jami’in kasar Ukiraniya ya bayyana cewa, a kalla mutane 8 ne su ka jikkata sanadiyyar munanan hare-haren da Rasha ta kai wa birnin Kiev ta hanyar amfani da makamai masu linzami.
Shugaban sha’anin tafiyar da Mulki na soja a birnin Kiev Taimur Tikatishinko ya wallafa sanarwa a shafinsa na “Telegram’ cewa; A tsakanin wadanda su ka jikkata din da akwai karamin yaro dan shekaru 3, kuma tuni an dauki mutane 4 zuwa asibiti, daya daga cikinsu yana cikin mummunan hali.
Shi kuwa magajin birnin na Kiev Fitali Kikitshiko cewa ya yi, mutanen da su ka jikkata suna zaune ne a cikin gidaje mabanbanta a unguwa daya.
Har ila yau ya kara da cea; Harin ya haddasa fashewa mai karfi wacce ta sa tagogin gidaje su ka fashe, har zuwa gine-gine masu hawa 11.
A wani labarin daga jami’an kasar ta Ukiraniya, Rasha ta kai wasu hare-haren da jirage marasa matuki a garin Kirofifitsky wanda ya haddasa fashewa mai yawa.
A cikin makwannin bayan nan dai Rasha ta tsananta kai hare-hare a fadin kasar Ukiraniya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuki.
Tun a 2022 ne dai Rasha ta fara kai wa Ukiraniya hare-hare bisa dalilin cewa tana son shiga cikin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato.
Kasar ta Ukiraniya dai tana samun taimakon makamai da bayanai na sirri daga kungiyar ta Nato.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
Sojojin mamayar Isra’ila sun yi furuci da halakar daya daga cikin sojojinsu sakamakon raunukan da ya samu a Zirin Gaza
Majiyar sojojin mamayar Isra’ila ta tabbatar a ranar Asabar din da ta gabata cewa: Wani soja ya mutu sakamakon raunukan da ya samu kwanakin baya -bayan nan sakamakon tashin bam a kan hanyar wata motar soji a zirin Gaza.
Tun da farko, sojojin mamayar Isra’ila sun amince da mutuwar Sajan Reserve Vladimir Loza, mai shekaru 36, daga matsugunin Ashkelon.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan gwagwarmayar Falastinawa ke ci gaba da kai hare-hare da kuma kwantan bauna kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila a fagage da dama a zirin Gaza, lamarin da ya janyo hasarar rayuka da na dukiyoyi ga ‘yan mamayar.
A ‘yan kwanakin da suka gabata, rundunar sojin Qassam bangaren sojin kungiyar Hamas ta bayyana a ta bakin kakakinta, Abu Obeida, cewa: Dabarunta a wannan mataki ita ce ta “kokarin halaka makiya, da gudanar da hare-hare masu inganci, da kuma neman kame sojoji a matsayin fursunonin yaki.