Leadership News Hausa:
2025-07-28@18:45:15 GMT

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

Published: 28th, July 2025 GMT

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

Jam’iyyar ta buƙaci hukumar INEC da sauran hukumomi da su lura cewa El-Rufai ba ɗan jam’iyyar ba ne, kuma bai da hurumin wakiltar ta a kowanne mataki. SDP ta kuma jaddada ƙudurinta na kare dimokuraɗiyya ta cikin gida da kuma adawa mai tushe da gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman

Shugabar riƙo ta jam’iyyar Labour (LP) ta ƙasa, Sanata Nenadi Usman, ta ce jam’iyyarsu ta shirya tsaf domin gyara manyan kura-kurai da gazawar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki ta jefa Nijeriya a ciki.

Sanata Usman ta bayyana hakan ne a wata ganawa da manema labarai a ƙarshen mako a Jihar Kaduna dangane da abinda da ke faruwa a cikin jam’iyyar LP.

Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila

Sanatar ta buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da goya musu baya domin a cewarta, jam’iyyar LP ce za ta farfaɗo da fatan da al’umma ke da shi da kuma ɗaga martabar ƙasar nan.

A cewarta, “Gwamnatin APC ta fi kowacce gwamnati a tarihin kasar nan jefa talakawan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa da fatara.”

Dangane da sauya sheƙa da ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, ciki har da wasu daga cikin ‘yan LP, Sanata Usman ta bayyana hakan a matsayin abin takaici, inda ta bayyana shi a matsayin abin kunya ne mutum ya samu nasara a cikin wata jam’iyya sannan ya canza sheƙa zuwa wata jam’iyyar.

Sai dai ta ce jam’iyyar LP ba ta damu da waɗannan sauya sheƙar ba, matuqar jama’ar ƙasa na tare da ita.

“Karfinmu yana fitowa ne daga goyon bayan talakawan Nijeriya, ba daga mahandama masu son kansu ba.”

Sanata Usman ta yarda cewa jam’iyyar ta aikata kura-kurai, musamman wajen tsayar da ‘yan takarar da ba su da cikakken fahimta ko biyayya ga manufofin jam’iyyar, amma ta tabbatar da cewa irin wannan kuskure ba zai maimaitu ba a nan gaba.

“Da yawa daga cikin waɗanda suka fice daga jam’iyyar tun farko ba su da cikakkiyar fahimta kan akidar gina sabuwar Nijeriya.

“Ficewarsu tana ƙara mana ƙwarin gwiwa kuma hakan yana fayyace mana masu kishin jam’iyyar na gaskiya,” inji ta.

Ta kuma buƙaci dukkan ‘ya’yan jam’iyyar da ke da saɓani da su rungumi sulhu su haɗa kansu yayin da jam’iyyar ke shirin ƙaddamar da sabunta rajistar mambobinta, gudanar da tarukan gunduma da na jihohi, da kuma babban taron ƙasa wanda tuni an samu amincewa daga Kwamitin Zartaswa na Kasa (NEC).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
  • An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar
  • HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna
  • Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
  • Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja
  • Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
  • LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman
  • Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar