Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi
Published: 28th, July 2025 GMT
Babban jami’in kungiyar Hamas a Zirin Gaza ya bayyana cewa: Makiya yahudawan sahayoniya suna rufe gazawar sojojinsu da kisan kare dangi
Khalil al-Hayya babban jami’in kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas a zirin Gaza ya jaddada cewa: Makiya yahudawan sahayoniyya suna rufe gazawar sojojinsu ta hanyar kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen hula.
A cikin wani jawabi kai tsaye ta gidan talabijin, Al-Hayya ya bayyana cewa: “Ya ku ‘ya’yan Dakarun Qassam, da na Quds Brigade, da kuma sauran kungiyoyin gwagwarmaya, abin da kuke yi ya kawo cikas ga farmakin da motoci masu sulke na makiya suke yi.
Khalil ya jaddada cewa: Babban hafsan hafsoshin sojin makiya yana rufe gazawar sojojinsa da kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen hulan Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta
A wani lamari makamancin haka da ya faru a Jihar Taraba, a watan Yuli, 2025, da misalin karfe 11:45 na rana, jami’an ‘yansanda sun amsa kiran da aka yi musu na satar mutane a hanyar Wukari, jim kadan a bayan jami’ar tarayya ta Wukari. Wata farar mota kirar Toyota bas dauke da fasinjoji 17 daga Enugu zuwa Yola, wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi musu kwanton bauna.
Jami’an ‘yansanda tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro sun yi gaggawar kai farmaki inda lamarin ya faru. Da ganin tawagar jami’an tsaro na zuwa, sai masu garkuwar suka yi bar wadanda abin ya shafa suka gudu cikin daji. An ceto dukkan fasinjoji 17 ba tare da jin rauni ba.
Sufeto-Janar na ‘yansanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya yaba da yadda jami’an ‘yansanda suka yi gaggawar daukar matakin. Ya sake nanata cewa rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ci gaba da jajircewa a kokarinta na wargaza hanyoyin sadarwar masu laifi a fadin kasar.
“Wadannan sakamakon da aka samu sun nuna irin kwarin gwiwar da rundunar ‘yansandan Nijeriya ta yi na kare lafiyar ‘yan kasa da kuma tsaron kasa,” in ji IGP, yana mai ba da tabbacin cewa za a ci gaba da gudanar da ayyukan da aka yi niyya tare da sabunta kwarin gwiwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp