Hukumar Tsarin Fansho na Hadin Gwiwa tsakanin Jiha da Kananan Hukumomi a Jihar Jigawa ta bayyana cewa ta raba sama da Naira Biliyan 1 da dubu 500 ga tsofaffin ma’aikata 569.

Yayin da yake jawabi ga wadanda suka ci gajiyar shirin a gaban Gidan Fansho kafin fara rabon kudin, Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K.

Dagaceri, ya bayyana tsarin fansho na jihar a matsayin daya daga cikin mafi nagarta a kasar nan.

A cewarsa, fiye da jihohi ashirin sun kai ziyara jihar Jigawa domin koyon yadda take tafiyar da shirin fansho.

Ya jinjina wa Gwamna Umar Namadi saboda dagewarsa da kuma jajircewarsa wajen dorewa da inganta tsarin fansho a jihar.

Alhaji Dagaceri ya yabawa Gwamna Namadi kan goyon bayansa da matakan da ya dauka tun bayan hawansa mulki domin inganta tsarin, yana mai jaddada irin tasirin alherin da shirin ke yi ga tsofaffin ma’aikata da daukacin ma’aikatan gwamnati.

Ya bukaci tsofaffin ma’aikata da wadanda ke aiki yanzu da su ci gaba da yi wa gwamnati addu’a, tare da nuna godiya ga Gwamna Namadi bisa irin ayyukan alherinsa.

A nasa jawabin, Shugaban hukumar ta Fansho, Dr. Binyaminu Shitu Aminu, ya bayyana cewa fiye da naira biliyan 1 da rabi ne za a raba tsakanin tsofaffin ma’aikata 569.

“Wannan adadi ya kunshi nau’o’in biyan kudi daban-daban, ciki har da hakkokin ritaya, hakkokin mutuwa da sauran ragowar hakkokin fansho na mamatan ma’aikata,” In ji Dr. Aminu.

Dr. Aminu ya kara da cewa, cikin wadanda za su amfana, 287 sun fito ne daga ma’aikatan jiha, 158 daga kananan hukumomi, yayin da 124 suka fito daga Hukumar Ilimin Kananan Hukumomi (LEA).

Ya kara da cewa, za a biya sama da Naira Miliyan 875 ga ma’aikatan da suka yi aiki a karkashin gwamnatin jiha, sannan sama da Naira Miliyan 355 kuma ga wadanda suka fito daga kananan hukumomi, da kuma sama da naira miliyan 274 ga wadanda suka fito daga LEA.

Shugaban hukumar ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da biyan hakkokin fansho a kan kari, ciki har da biyan fansho na wata wata a cikin mako na farko na kowane wata.

 

Ya jaddada kudurin gwamnatin jihar na inganta walwalar ma’aikata, domin samun rayuwa mai kyau da kwanciyar hankali bayan kammala aikin.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: sama da Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Tsofaffin Gwamnoni Sun Ziyarci Tinubu Tare Da Bashi Shawarwari Kan Matsalolin Tsaro

Tsoffin gwamnoni da suka fara mulki a shekarar 1999, da ake kira “Class of ’99,” sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadar Gwamnati da ke Abuja a ranar Juma’a, inda suka gabatar da shawarwari na aiki domin magance matsalolin tsaro, inganta tattalin arziki da kuma samar da ayyukan yi a fadin ƙasar.

Tawagar, ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Jihar Edo, Lucky Igbinedion, ta haɗa da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), George Akume, da wasu tsoffin gwamnoni da suka yi mulki tare da Shugaba Tinubu lokacin da yake Gwamnan Jihar Lagos.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan ganawar da ta ɗauki fiye da awa guda, Igbinedion ya bayyana cewa ziyarar tasu na da nufin yin wata ganawa da ɗan ajinsu kuma su tattauna hanyoyin da za a ciyar da ƙasa gaba.

“Mun zo ganin takwaranmu, wanda muka fara mulki tare a shekarar 1999, don tattauna batutuwan da ke da muhimmancii ga ƙasa. Mun tattauna kan batun tsaro, tattalin arziki, noma da samar da ayyukan yi. Shugaban ya nuna damuwa matuƙa kan waɗannan matsaloli, kuma ya karɓi shawarwarinmu da hannu biyu.” In ji shi.

Igbinedion ya jaddada cewa tsaro ya kamata ya kasance babban fifiko na gwamnati, domin ba za a samu ci gaba ba tare da zaman lafiya idan ba tsaro ba.

Game da batun ayyukan yi, tsohon gwamnan ya yi kira da a kafa masana’antu kanana (cottage industries) a kowace ƙaramar hukuma a matsayin hanyar dorewar rage rashin aikin yi da fatara.

“In har za ka ba mutum tallafi yau, me zai faru gobe? Mun roƙi Shugaban Ƙasa da ya kafa ƙanana masana’antu a faɗin ƙasa domin mutane su samu ayyukan yi.” In ji shi.

Tawagar ta yaba wa Shugaba Tinubu bisa maraba da shawarwari masu amfani, inda suka ce Shugaban Ƙasar ya tabbatar musu da cewa zai yi la’akari da duk wani tunani mai amfani da zai ciyar da ƙasa gaba.

“Shugaban Ƙasa ya tabbatar mana cewa ƙofofinsa a bude suke don tattaunawa da shawarwari masu amfani da za su inganta ƙasar nan.” In ji Igbinedion.

Wannan shi ne karo na biyu da tsoffin gwamnoni na  1999 ke ziyartar Shugaban Ƙasa Tinubu tun bayan hawansa mulki.

 

Bello Wakili

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
  • Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
  • Tsofaffin Gwamnoni Sun Ziyarci Tinubu Tare Da Bashi Shawarwari Kan Matsalolin Tsaro
  • Manoma A Kirikasamma Sun Yaba Wa Gwamna Namadi Bisa Rangwaman Takin Zamani
  • Burtaniya Zata Fara Jefawa Falasdinawa Abinci Daga Sama
  • Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa