More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

’Yan Najeriya da dama ne dai aka bayyana ba sa fitowa kaɗa kuri’a a duk lokacin da zaɓe ya zagayo.

Wasu daga cikin ’yan ƙasar sun bayyana rashin jin daɗin abun da hukumar zaɓe ke yi, rashin yarda da sakamakon zaɓuɓɓukan da suka gabata da dai sauransu a matsayin dalilansu na rashin kaɗa ƙuri’a.

Ko waɗanne matakai Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) take ɗauka don ƙarfafawa ’yan Najeriya gwiwan fitowa su kada ƙuri’a a zaɓen 2027?

NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

 Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza

A daidai lokacin da aka cika kwanaki 659 daga fara kisan kiyashin Gaza, sojojin Sahayoniya suna ci gaba da killace yankin da hana shigar da abinci da magani.

Ma’aiktar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa ya zuwa wannan lokacin jumillar wadanda yunwa ta kashe sun kai 122 daga cikinsu da akwai kananan yara 83.

Da jijjifin safiyar yau Asabar, majiyar asibitin “Nasr’ ta sanar da cewa wata jaririya ta yi shahada saboda rashin abinci mai gina jiki. Haka nan kuma ta ce, jaririyar ‘yar watanni 6 da haihuwa ta yi shahada ne saboda rashin abinci mai gina jiki da kuma magani saboda takunkumin da HKI ta kakabawa yankin na Gaza.

Babban jami’iin gudanarwa na ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza Dr. Munir al-Bursh ya sanar da cewa; Ana kara samun masu mutuwa saboda yunwa, musamman ma dai a tsakanin kananan yara.

Al-Bursh ya fada wa tashar talabijin din al-jazira cewa; Yunwa saboda rashin abinci da kuma rashin Magani ya sa jariran da suke cikin  mata 3,000 sun mutu.

Haka nan kuma ya nuna mamakinsa akan yadda duniya ta gajiya wajen iya shigar da madarar jarirai cikin yankin Gaza domin ceto da rayuwar kananan yara da jarirai.

A wannan tsakanin ne dai Asusun kananan yara na MDD ( Unicef) ya yi gargadi akan mummunan halin da yaran Gaza suke ci gaba da shiga saboda rashin abinci mai gina jiki.

Ita kuwa shugabar hukumar Agaji ta kasa da kasa “Rd Cross” ta yi kira ne da a kawo karshen wahalhalu da bala’in da aka jefa mutane a Gaza, cikin gaggawa ba tare da ba ta lokaci ba.

A wani labarin na daban, kafafen watsa labarun HKI sun ce, sojojin Sahayoniya sun lalata tarin abinci mai yawa da aka ware domin shigar da shi zuwa yankin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Kungiyar Kwallon Kafa Ta Matan Najeriya Ta Samu Nasara Akan Takwararta Ta Moroko Da Kwallaye 3-2
  • Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
  • Musulmi A Amurka Sun Fara Daukar Matakan Tsaro A Masallatai Saboda Makiya
  • Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
  •  Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza
  • An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi