Aminiya:
2025-07-28@18:42:52 GMT

Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000

Published: 28th, July 2025 GMT

Gwamnatin Najeriya ta ba wa ƙasar Habasha kyautar itatuwan cashew guda 2,000 da kuma irin cashew guda 100,000.

Najeriya ta bayar da kyautar irin ne a wani bangare na yunƙurin taimaka wa ƙasashen biyu wajen samar da abinci mai yawa da kuma ƙarfafa dangantakarsu.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya bayar da wannan kyauta, da za ta iya shuke ƙasa mai fadin hekta 600.

Shettima ya bayar kyautar ce a lokacin da ya isa birnin Adis Ababa, babban birnin kasar, domin halartar Babban Taron Majalisar Xinkin Duniya Kan Tsarin Abinci.

Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja

Ministan Harkokin Noma na Habasha, Dakta Efa Muleta Boru, ya karbi kyautar, a matsayin wani bangare na shirin ƙasashen biyu na taimakon juna a fannin noma.

A watan Yuni na 2025, kasar Habasha ta ba wa Najeriya itatuwan avocado da na kofi.

Wannan kokari yana goyon bayan shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na inganta noma a Najeriya.

Haka kuma yana nuna cewa Najeriya na son amfani da “Diflomasiyyar Juyin Juya Halin Kore” don gina kyakkyawar dangantaka da sauran kasashe tare da magance matsalolin samar da abinci.

Mataimakin Shugaban Kasa zai gana da sauran shugabannin duniya a taron domin tattauna yadda za a inganta samar da abinci a duniya. Zai kuma halarci wasu tarurrukan don musayar ra’ayoyi da kulla kawance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo
  • Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC
  • Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo
  • Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
  • Burtaniya Zata Fara Jefawa Falasdinawa Abinci Daga Sama
  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA