An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
Published: 29th, July 2025 GMT
Yau Litinin, an gudanar da taron dandalin tattaunawar neman sabon tunani na asali na 2025 a birnin Hangzhou dake lardin Zhejiang. Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, Li Shulei, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi.
Mahalarta taron sun bayyana cewa, ya kamata mu ci gaba da sa kaimi ga yin gyare-gyare da kirkire-kirkire yayin bunkasa al’adun gargajiya na kasar Sin, da kuma nuna kimar kasar Sin da karfin wayewar kai da al’adu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Zanga-Zangar Nuna Goyon Baya Ga Al’ummar Falasdinu A Birnin Tunis Fadar Mulkin Kasar Tunusiya
An gudanar da gagarumin tattaki a kasar Tunisiya domin nuna adawa da yunwar da aka kakaba wa al’ummar Falasdinu a Gaza
Masu zanga-zangar Tunusiya a wani gagarumin tattaki da suka gudanar a tsakiyar babban birnin kasar, sun tabbatar da goyon bayansu ga gwagwarmayar Falasdinawa tare da bayyana cewa shiru da duniya ta yi kan killace Gaza da aka shafe sama da kwanaki 140 ana yi, abu ne da ba za a amince da shi ba.
A ci gaba da nuna goyon baya ga yunkurin da kasashen duniya ke yi na yaki da yunwa a zirin Gaza da aka killace, al’ummar Tunisiya sun fito kan tituna suna gudanar da gagarumin jerin gwano, suna daga tutar kungiyoyin ‘yan gwagwarmaya da kuma rera wakokin adawa da shirun Larabawa da na sauran kasashen duniya dangane da wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya ke ci gaba da yi, da rufe mashigin ruwa, da kuma hana kai kayan agajin sama da kwanaki 140.
Mohsen Nabti, kakakin jam’iyyar Popular Current, ya shaidawa tashar talabijin ta Al-Alam cewa: “Mafi ƙanƙantan matakin da ya dace shi ne yanke duk wata alaka da yahudawan sahayoniyya, kuma mafi ƙanƙanta taimako ga al’ummar Falasdinu shi ne a ɗage killacewar da aka yi wa musu, sannan mafi ƙaramar hukunta ‘yan mamaya shi ne kauracewa kasuwanci da maƙiyan yahudawan sahayoniya.
Masu zanga-zangar a titin Habib Bourguiba da ke birnin Tunis sun yi ta rera taken nuna goyon baya ga ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa da kuma yin kira da a ci gaba da matsin lambar al’ummomin duniya don tilasta wa makiya dakatar da kisan gillar da suke yi wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a Gaza.